ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abincin Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Ci Da Wanda Bai Kamata Ba

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Azumi

Assalamu alaikum barkanmu da warhaka, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin wata mai alfarma na Ramadan a cikin shirin namu na Girki Adon Mata.

 Watan Azumi lokaci ne da musulmi ke kaurace wa abinci tun kafin ketowar alfijir har zuwa faduwar rana. Hakan yake sa mutane jin yunwa da gishin ruwa. Masu Azumi sukan ci abinci daban-daban a lokacin sahur da na buda baki.

  • “Tutar Dimokuradiyya” Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace
  • Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

Sai dai likitoci sun bayyana nau’in abincin da ya kamata mai Azumi ya ci da wanda ya kamata ya kauracewa.

ADVERTISEMENT

 Dakta Lawan Musa Tahir, wani likita a asibitin Nizamiye da ke Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, ya shaida wa BBC Hausa irin abincin da ya kamata masu Azumi su ci da kuma wadanda ba su kamata ba.

Wanne nau’in abinci ya kamata mai Azumi ya ci?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

Masu fama da wasu cututtuka

 Masu Azumi sun kasu kashi-kashi: misali, akwai wanda da ma kafin Azumin saboda da wata larura a asibiti za a dora shi kan abincin da ya kamata ya ci ko kada ya ci.

Misali a nan shi kamar wanda yake da ciwon suga za a dora shi kan dokoki na yanayin abincin da zai ci, ko wanda yake da ciwon hanta, shi ma za a dora shi kan dokoki na abinci da zai ci, sai mai olsa shi ma akwai abubuwan da ya kamata ya ci da kuma wanda bai kamata ba.

 Haka kuma wanda yake da ‘food allergy’, wato wanda jikinsa ba ya karbar wasu nau’o’in na abinci: To, kun ga wannan tun kafin Azumi akwai dokoki na yanayin abincin da yake ci, don haka idan Azumi ya zo zai ci gaba da bin dokokin.

Mutanen da suke koshin lafiya

Sai kuma mutanen da su da ma lafiyarsu kalau, su ma ya danganta da inda suka samu kansu lokacin Azumi.

 Misali, idan mutum yana zaune a irin kasashenmu masu zafi inda mutane suke bukatar yawan shan ruwa a kai – a kai, su ma akwai yadda ya kamata su yi. Ga jerin abinci da abubuwan da suka kamata masu Azumi  su yi:

Guji cin abinci mai yaji da wanda yake da maiko sosai saboda zai kara musu kishirwa sannan akwai zafin gari. A ci abinci mai ruwa-ruwa, musamman ‘ya’yan itatuwa irin su Ayaba, Abarba, Gwanda, Kankana da makamantansu

A sha ruwan zafi kamar shayi ko koko ko kunu domin suna gyara ciki musamman bayan an dade ba a ci abinci ba. A guji cika ciki fal da abinci za ka ga wasu suna cin abinci sosai idan an sha ruwa. Hakan yana da matsala. An fi so ka ci abinci kadan sannan ka huta yadda idan an jima za ka iya sake ci.

 A guji shan taba da dangoginta saboda tana da illa. Babu laifi idan an motsa jiki lokacin Azumi amma a yi shi saisa-saisa.

Azumi
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasihar Da Ya Dace Dukkan Iyaye Su Yi Wa ‘Yaƴansu Yayin  Aure?
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Abin Da Yake Kashe Matanmu Na Hausawa

MASU ALAKA

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
Girke-Girke

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Amfanin Man Kwakwa Guda 12
Girke-Girke

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

May 17, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Girke-Girke

Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada

May 10, 2026
Next Post
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.