ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abincin Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Ci Da Wanda Bai Kamata Ba

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Azumi

Assalamu alaikum barkanmu da warhaka, barkanmu da sake haduwa da ku a wannan makon a cikin wata mai alfarma na Ramadan a cikin shirin namu na Girki Adon Mata.

 Watan Azumi lokaci ne da musulmi ke kaurace wa abinci tun kafin ketowar alfijir har zuwa faduwar rana. Hakan yake sa mutane jin yunwa da gishin ruwa. Masu Azumi sukan ci abinci daban-daban a lokacin sahur da na buda baki.

  • “Tutar Dimokuradiyya” Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace
  • Tsaron Iyakoki: ACG James Sunday Ya Jagoranci Taron Samar Da Dabarun Aiki A Jos

Sai dai likitoci sun bayyana nau’in abincin da ya kamata mai Azumi ya ci da wanda ya kamata ya kauracewa.

ADVERTISEMENT

 Dakta Lawan Musa Tahir, wani likita a asibitin Nizamiye da ke Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeriya, ya shaida wa BBC Hausa irin abincin da ya kamata masu Azumi su ci da kuma wadanda ba su kamata ba.

Wanne nau’in abinci ya kamata mai Azumi ya ci?

LABARAI MASU NASABA

Tuwon Alkama Da Miyar Taushe

Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna

Masu fama da wasu cututtuka

 Masu Azumi sun kasu kashi-kashi: misali, akwai wanda da ma kafin Azumin saboda da wata larura a asibiti za a dora shi kan abincin da ya kamata ya ci ko kada ya ci.

Misali a nan shi kamar wanda yake da ciwon suga za a dora shi kan dokoki na yanayin abincin da zai ci, ko wanda yake da ciwon hanta, shi ma za a dora shi kan dokoki na abinci da zai ci, sai mai olsa shi ma akwai abubuwan da ya kamata ya ci da kuma wanda bai kamata ba.

 Haka kuma wanda yake da ‘food allergy’, wato wanda jikinsa ba ya karbar wasu nau’o’in na abinci: To, kun ga wannan tun kafin Azumi akwai dokoki na yanayin abincin da yake ci, don haka idan Azumi ya zo zai ci gaba da bin dokokin.

Mutanen da suke koshin lafiya

Sai kuma mutanen da su da ma lafiyarsu kalau, su ma ya danganta da inda suka samu kansu lokacin Azumi.

 Misali, idan mutum yana zaune a irin kasashenmu masu zafi inda mutane suke bukatar yawan shan ruwa a kai – a kai, su ma akwai yadda ya kamata su yi. Ga jerin abinci da abubuwan da suka kamata masu Azumi  su yi:

Guji cin abinci mai yaji da wanda yake da maiko sosai saboda zai kara musu kishirwa sannan akwai zafin gari. A ci abinci mai ruwa-ruwa, musamman ‘ya’yan itatuwa irin su Ayaba, Abarba, Gwanda, Kankana da makamantansu

A sha ruwan zafi kamar shayi ko koko ko kunu domin suna gyara ciki musamman bayan an dade ba a ci abinci ba. A guji cika ciki fal da abinci za ka ga wasu suna cin abinci sosai idan an sha ruwa. Hakan yana da matsala. An fi so ka ci abinci kadan sannan ka huta yadda idan an jima za ka iya sake ci.

 A guji shan taba da dangoginta saboda tana da illa. Babu laifi idan an motsa jiki lokacin Azumi amma a yi shi saisa-saisa.

Azumi
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Tuwon Alkama Da Miyar Taushe
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kula Da Labba Domin Su Kasance Masu Laushi
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Kare Hannu Daga Bushewa

MASU ALAKA

Tuwon Alkama Da Miyar Taushe
Girke-Girke

Tuwon Alkama Da Miyar Taushe

September 5, 2026
Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
Girke-Girke

Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna

August 29, 2026
Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice
Girke-Girke

Yadda Ake Chicken Teriyaki Rice

August 29, 2026
Next Post
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.