• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abokin Da Ke Iya Ba Ka Taimako A Lokacin Da Kake Bukata, Shi Ne Aboki Na Kwarai

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Abokin Da Ke Iya Ba Ka Taimako A Lokacin Da Kake Bukata, Shi Ne Aboki Na Kwarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai nisan kimanin kilomita dubu 10 tsakanin Kenya da kasar Sin, to, amma ko kun san tsawon lokacin da aka dauka wajen jigilar wani furen rose da aka tsinta daga gonar da ke kasar ta Kenya zuwa kasar Sin?

 

Allah ya hore wa kasar Kenya albarkatun furanni irinsu Rose, har ma kasar ta kasance kasar da ta fi yawan fitar da furanni zuwa ketare a nahiyar Afirka. Sai dai a baya, a kan shafe tsawon kwanaki uku kafin a kai furannin kasar Kenya kasuwannin kasar Sin, lokacin da ya yi matukar raguwa zuwa sa’o’i 17 kawai a yanzu.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Amma me ya haifar da wannan babban sauyi mai ban mamaki? Amsa ita ce matakan da kasar Sin ta yi ta dauka na inganta hadin gwiwarta da kasashen Afirka ta fannin cinikayya. Idan ba mu manta ba, a watan Nuwamban shekarar 2021, gwamnatin kasar Sin ta sanar da samar da matakai masu sauki kan amfanin gona da ke shigowa daga kasashen Afirka, inda ta rage tsawon lokaci na binciken cututtuka da ma fadada kayayyakin da ake cire musu harajin kwastam da sauransu, matakan da suka fadada hanyoyi zuwa kasuwannin kasar Sin ga amfanin gonar kasashen Afirka, ciki har da furannin kasar Kenya da Avokado da lemo da Abarba da sauransu. Ya zuwa watan Yunin bara, akwai nau’o’in amfanin gona 16 na kasashen Afirka 11 da kasar Sin ta shigo da su kasuwanninta sakamakon matakan, an kuma cire harajin kwastam a kan kaso 98% na kayayyakin da kasar Sin ta shigo daga wasu kasashen Afirka 21.

 

Labarai Masu Nasaba

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Ban da haka, kasar Sin ta kuma kafa bikin baje kolin kayayyakin da take shigowa da su kasa da kasa, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka da musamman ta kafa domin kasashen Afirka, da sauransu, don yayata kayayyakin kasashen Afirka a kasuwanninta.

 

Cinikin waje na daya daga cikin manyan gishikai uku da ke samar da bunkasar tattalin arziki, don haka ma kullum ake saka batun bunkasa ciniki a matsayin daya daga cikin muhimman fannoni na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Bisa ingantattun matakan da aka ta dauka a gun tarurukan dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya yi ta bunkasa tare da haifar gaggaruman nasarori, inda a cikin shekaru 15 a jere, kasar Sin ta kasance abokin cinikayya mafi girma ga nahiyar Afirka, a bara kuma, jimillar ciniki a tsakanin sassan biyu har ta kai wani matsayin tarihi na dala biliyan 282.1.

 

Sakamakon makamancin abin da ya faru gare su a tarihi da ma buri daya da suke neman cimmawa, kasar Sin ta san mene ne aminanta na Afirka ke fatan cimmawa, don haka ma take son raba damammaki da su don tabbatar da hadin gwiwar cin moriyar juna.

 

Kamar yadda bature kan ce, abokin da ke iya ba ka taimako a lokacin da kake bukata, shi ne aboki na kwarai. Abin haka yake, wanda kuma hakan ya shaida huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka.(Mai zane:Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Darajar Naira: Tsohon Dan Majalisa Da Ya Ci Bashin Karatu N1,200 A Shekaru 47, Yanzu Ya Biya Da Fiye Da Naira Miliyan 3

Next Post

Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

Related

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

17 hours ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

2 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

7 days ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 weeks ago
Next Post
Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.