• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abokin Da Ke Iya Ba Ka Taimako A Lokacin Da Kake Bukata, Shi Ne Aboki Na Kwarai

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Aboki

Akwai nisan kimanin kilomita dubu 10 tsakanin Kenya da kasar Sin, to, amma ko kun san tsawon lokacin da aka dauka wajen jigilar wani furen rose da aka tsinta daga gonar da ke kasar ta Kenya zuwa kasar Sin?

 

Allah ya hore wa kasar Kenya albarkatun furanni irinsu Rose, har ma kasar ta kasance kasar da ta fi yawan fitar da furanni zuwa ketare a nahiyar Afirka. Sai dai a baya, a kan shafe tsawon kwanaki uku kafin a kai furannin kasar Kenya kasuwannin kasar Sin, lokacin da ya yi matukar raguwa zuwa sa’o’i 17 kawai a yanzu.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
  • Inganta Raya Shawarar BRI Zai Zama Daya Daga Manyan Batutuwan Da Za A Tattauna A Gun Taron Kolin FOCAC Na Bana

Amma me ya haifar da wannan babban sauyi mai ban mamaki? Amsa ita ce matakan da kasar Sin ta yi ta dauka na inganta hadin gwiwarta da kasashen Afirka ta fannin cinikayya. Idan ba mu manta ba, a watan Nuwamban shekarar 2021, gwamnatin kasar Sin ta sanar da samar da matakai masu sauki kan amfanin gona da ke shigowa daga kasashen Afirka, inda ta rage tsawon lokaci na binciken cututtuka da ma fadada kayayyakin da ake cire musu harajin kwastam da sauransu, matakan da suka fadada hanyoyi zuwa kasuwannin kasar Sin ga amfanin gonar kasashen Afirka, ciki har da furannin kasar Kenya da Avokado da lemo da Abarba da sauransu. Ya zuwa watan Yunin bara, akwai nau’o’in amfanin gona 16 na kasashen Afirka 11 da kasar Sin ta shigo da su kasuwanninta sakamakon matakan, an kuma cire harajin kwastam a kan kaso 98% na kayayyakin da kasar Sin ta shigo daga wasu kasashen Afirka 21.

 

LABARAI MASU NASABA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Ban da haka, kasar Sin ta kuma kafa bikin baje kolin kayayyakin da take shigowa da su kasa da kasa, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka da musamman ta kafa domin kasashen Afirka, da sauransu, don yayata kayayyakin kasashen Afirka a kasuwanninta.

 

Cinikin waje na daya daga cikin manyan gishikai uku da ke samar da bunkasar tattalin arziki, don haka ma kullum ake saka batun bunkasa ciniki a matsayin daya daga cikin muhimman fannoni na hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka. Bisa ingantattun matakan da aka ta dauka a gun tarurukan dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da kasashen Afirka ya yi ta bunkasa tare da haifar gaggaruman nasarori, inda a cikin shekaru 15 a jere, kasar Sin ta kasance abokin cinikayya mafi girma ga nahiyar Afirka, a bara kuma, jimillar ciniki a tsakanin sassan biyu har ta kai wani matsayin tarihi na dala biliyan 282.1.

 

Sakamakon makamancin abin da ya faru gare su a tarihi da ma buri daya da suke neman cimmawa, kasar Sin ta san mene ne aminanta na Afirka ke fatan cimmawa, don haka ma take son raba damammaki da su don tabbatar da hadin gwiwar cin moriyar juna.

 

Kamar yadda bature kan ce, abokin da ke iya ba ka taimako a lokacin da kake bukata, shi ne aboki na kwarai. Abin haka yake, wanda kuma hakan ya shaida huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka.(Mai zane:Mustapha Bulama)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Next Post
Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

Muhalli Mai Kyau Na Kasar Sin Ya Sake Dawo Da Giwaye

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.