• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abu Bilal: Farfesan Da Ke Sana’ar Walda A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Abu Bilal

Farfesa Kabir Ahmed da ake yi wa laKabi da Abu Bilal ya bambanta da sauran Farfesoshi a Nijeriya, wadanda ke dogara kawai da sana’ar koyarwa a jami’o’i, shi a nasa bangare yana gudanar da sana’ar walda a matsayin sana’a ta biyu a garin Zariya da ke arewacin kasar.

Ana kallon sana’ar walda a matsayin karamar sana’a musamman a Nijeriya, lamarin da ya sa labarinsa ya bai wa mutane da dama mamaki, musamman abokan sana’arsa, bayan ya bude warin gudanar da sana’ar.

  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi
  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma

“Bana jin wata shakkar kasancewata mai walda duk da cewa ni Farfesa ne, saboda ina samun kudi ta hanyar sana’ar,” kamar yadda ya bayyana wa BBC.

Malamin jami’ar mai shekara 50 – wanda ke duba daliban da ke bincike a tsangayar koyar da injiniyanci a jami’ar Ahmadu Bello da Zariya, ya kwashe shekara 18 yana koyarwa tare da wallafe-wallafen littafai.

Abu Bilal ya ce yana da kyau mutane, musamman wadanda suka kammala karatu, su rika fadada tunaninsu kan yadda za su samu abin dogaro da kawunansu.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

“Ilimi ba zai hana ka gudanar da irin wadannan sana’o’i ba, na yi mamakin yadda mutane musamman wadanda ke da digiri na farko ke kallon irin wadannan sana’o’i a matsayin kankanci.”

Kalamansu sun yi daidai da wani rahoto da ya ce fiye da kashi 40 na wadanda ke kammala jami’a ba sa samun aikin gwamnati a Nijeriya, kasar da ta fi kowace yawan al’umma a nahiyar Afirka.

Malamin ya bude wani karamin wajen walda a Zariya kusan shekara 20 da suka gabata.

A shekarar 2022, shekara guda bayan ya zama farfesa, ya koma wani sabon wur mai girma, inda ya bude sana’o’i masu yawa a garin.

Hakan ya ba shi damar sayo karin kayan aiki masu yawa, tare da gudanar da manyan ayyuka, inda kwastomominsa ke zuwa don yi musu abubuwa kamar kofar karfe da tagogi da sauran abubuwa.

“Na kan yi sana’a komai kankantarta, ko da kofa guda ce nakan yi mata walda cikin jin dadi domin a biyani,’” in ji shi.

Tun yana matashi, Farfesan ya ce yake ta sha’arwar gyaran abubuwa irinsu radiyo, lamarin da ya kai shi ga karatun fanin injiniya, “Sai dai abin mamakin, sai na fahimci injiniyanci da ake koyarwa a jami’a a takarda ne kawai, don haka ina bukatar wurin da yi rika aiwatar da shi a aikace,” in ji shi

Wannan sha’arwa ce ta sa na bude shago don fara walda’”.

Ba wai don cika burinsa ne kawai ya bude shagon ba, sana’ar na taimaka masa wajen samun abin biyan bukatunsa na yau da kullum.

Farfesa Abu Bilal ya ce sana’arsa ta walda na ba shi damar samun abin biyan bukatunsa, lamarin da ya sa har ya samu damar sayen karamar motarsa mai kyau kirar ‘Mercedes’.

“A lokacin da malaman jami’a muka tsunduma yajin aiki na kusan wata takwas a shekarar 2022, kuma gwamnati ta daina biyanmu albashi, ban rasa abin kashewa ba saboda wannan sana’ar, kuma wasu daga cikin takwarorina kan zo wajen domin in taimaka musu’”.

Farfesa Abu Bilal na fatan jan ra’ayin sauran mutane irinsa da su rungumi sana’o’i irin nasa. Yana da yara 10 a shagon masu shekaru tsakanin 12 zuwa 20, da ke samun kwarewa kan sana’ar a wajen shehin malamin jami’ar.

Wadanda ba su je makaranta da rana ba, ke kula da shagon da rana idan malamin yana jami’ar.

Masu koyon sana’ar kan yi shekara guda a shagon Farfesan – sannan su je su bude nasu wuraren sana’ar bayan ya yayesu

“Na koyi abubuwa da dama a wurin, a yanzu ina iya yin abubuwa masu yawa ta hanyar walda,” in ji wani matashi mai shekara 18 da ke koyon sana’ar a wurin.

“Duk da cewa mu masu koyon sana’a ne, yana ba mu naira 10,000 a kowane wata, baya ga kudin abinci da yake ba mu a kowacce rana”.

Shehin malamin jami’ar ya kuma ce yana fatan ‘ya’yansa biyar su koyi sana’r tasa domin dagora da kawunansu, “Nakan zo da su wajen sana’ar a ranakun da babu makaranta domin su ga yadda ake gudanar da wannan sana’ar, ina so su koyi sana’ar saboda wata rana”.

A ganin Farfesa Abu Bilal wannna sana’ar tasa ba za ta hana shi sauke nau’in koyarwa da yake yi a jami’a ba, saboda shi ma aikin koyarwa aiki ne da yake da sha’awarsa sosai ”Ina son koyar da ilimi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Yawan Katsewar Network Na Haifar Mana Da Koma-baya A Harkar Kasuwanci – Masu POS

Yawan Katsewar Network Na Haifar Mana Da Koma-baya A Harkar Kasuwanci – Masu POS

LABARAI MASU NASABA

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.