ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawan Katsewar Network Na Haifar Mana Da Koma-baya A Harkar Kasuwanci – Masu POS

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Network

Masu sana’ar hada-hadar kudi na POS a Nijeriya sun koka kan yawaitar katsewar network din layukan waya daga kamfanonin sadarwa a Nijeriya inda suka misalta hakan a matsayin hanyoyin da ke janyo wa harkar kasuwancinsu koma baya.

Na’urar POS dai ya zama wani hanya mafi sauki da jama’a ke runguma wajen yin hada-hadar kudade kama daga shigar da kudadensu ko cirewa. Hakan kuma ya biyo bayan wahalar zuwa bankuna ko na’urar cirar kudi na ATM da jama’a ke fuskanta.

  • Amurka Na Dauke Da Nauyin Dakatar Da Kisan Fararen Hula A Rafah
  • Matsalar Tsaro A Nijeriya: Akwai Bukatar Daukar Kwakkwaran Mataki

A Nijeriya masu sana’ar POS wadanda mafi yawansu matasa ne sun kasance masu shiga tsakanin bankuna da kwastomomi inda suke saukaka wa bankuna matsalolin hulda da kudade.

ADVERTISEMENT

A ‘yan kwanakin nan an yi ta fuskanta matsalolin da suka shafi na katsewar network daga kamfanonin sadarwa, inda masu POS suka nuna hakan a matsayin babban matsala da ke kawo musu cikas.

Wani mai sana’ar POS a jihar Bauchi, Sulaiman Alhassan ya shaida wa shafin Kimiyya da fasaha cewa, “A ‘yan kwanakin nan muna fuskantar matsalolin network gaskiya. Har ta kai idan mutum na son kada ya rasa kwastomomi yadda yake so ko yadda ya saba to dole sai ya sayi data a layuka a kalla uku, idan wannan kamfanin ya katse sai ya canza zuwa wani kamfanin sadarwa, to matsalar da muke fuskanta ko a hakan ne ma, idan kwastoma ya zo kana kokarin canza layi zuwa wani domin ka samu karfin network din da za ka tura ko cire wa kwastoma kudi, a nan gabar sai hakurin mutum ya kare ka ga ya nemi wucewa zuwa wani wajen.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

“Na rasa kwastomomi sosai a irin wannan. Kuma dai daman cinikin ma ya ragu amma sakamakon matsalar network gaskiya muna rasa ciniki matuka.”

“Amma idan mutum ya dage yana da layuka da yawa kamar uku, duk da hakan ma asara muke yi, misali, idan zan sanya datar MTN na dubu uku na ci gaba da tura kudi ko cirewa, sai ya zama a kowani rana ina fargabar network zai iya dauke min, zan kuma sake wani datar dubu uku a zain ko glo ka ga ko ba komai na sake kashe wani kudin a wani abun da ban tsara yi ba.

“A zahiri yawaitar katsewar network na janyo mana cikas da matsaloli,” ya shaida.

Kazalika, wata mai sana’ar POS Mary Daniel daga jihar Gombe ta shaida cewar, “Layi daya nake amfani da shi, duk lokacin da network ya yanke sai dai na zauna na yi ta kallo. Babbar matsalar da muke fuskanta idan network din nan na yawa, za mu iya tura kudi ya zo bai je ba ko kuma ya fita bai nuna mana ba. Don haka a irin wannan fargabar kamar mu masu karamin karfi kawai na kan gwammace na hakura da cigaba da kasuwancin har sai an samu network mai karfi kafin na cigaba da yin kasuwancina. A hakan kuma asara kawai muke yi da bata lokaci,” ya shaida.

Network
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen ‘Yan ta’adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

Hedikwatar Tsaron Nijeriya Ta Bayyana Sunayen 'Yan ta'adda 97 Da Ake Nema Ruwa A-jallo

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.