• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Gabon 

by Sadiq
2 years ago
Gabon

Gabon, Kasa ce da ke Yammacin gabar tekun Afirka ta Tsakiya, sannan kasa ce da Allah ya albarkace ta da yalwar dazuka da kuma namun daji iri daban-daban, sannan suna da sadaukar da kai don ci gabansu.

Kazalika, Gabon kasa ce da ta ke da burin dorewa a matsayin kasa don samun ci gaba mai dorewa, da nufin kare albarkatun kasa tare da bunkasa tattalin arzikinta.

  • Sojojin Gabon Sun Kama Dan Hambararren Shugaban Kasa Da Laifin Cin Amanar kasa.
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Gabon

Har zuwa safiyar ranar Laraba, Gabon ta kasance karkashin mulkin Shugaba Bongo tun shekarar 1967.

Hambararren shugaba Ali Bongo Ondimba ya kasance dan marigayi Omar Bongo, wanda shi ne shugaban kasar Gabon na biyu daga shekarar 1967 har zuwa mutuwarsa a shekarar 2009.

Bayan mutuwar mahaifinsa, Ali Bongo ya lashe zaben shugaban kasar Gabon na 2009, inda ya zama shugaban kasar na uku.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

An sake zabensa a shekarar 2016, a zabukan da aka yi mai cike da cece-kuce na rashin bin ka’ida, take hakkin dan Adam, da zanga-zangar bayan zabe da tashin hankali.

An kuma ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben 2023 na Gabon mai cike da cece-kuce. A ranar 30 ga watan Agusta, 2023 ne dakarun sojin Gabon suka yi juyin mulki na biyu a tarihin Gabon tun bayan samun ‘yancin kan kasar a shekarar 1960, inda suka yi juyin mulki na farko a shekarar 1964.

Abubuwa 10 na musamman game da Gabon:

1. Yalwar Dazuka: Gabon tana alfahari da yawan dazuka a kasar, wanda hakan ke taimaka mata wajen bunkasa tattalin arzikinta.

2. Mayar Da Hankali Kan Ci Gaba: Ƙasar ta himmatu wajen samar da ci gaba mai dorewa, ta hanyar kebe wani yanki mai yawa na kasart matsayin wuraren shakatawa kamar irin su Loango National Park, wanda ke ba da kariya ga namun daji da sauran wuraren shakatawa da ke bakin teku.

3. Bambance-bambancen Al’adu: Gabon kasa ce mai kabilu sama da 40, kowannensu yana da al’adunsa da harsuna daban-daban.

4. Manyan Namun Daji: Kasa mai tarin manyan namun daji kamar irin su giwaye, gwaggon biri, macizai da sauransu.

5. Wuraren Shakatawa: Wannan ya kunshi muhimman wuraren shakatawa da masu yawon bude ido ke zuwa wanda yawanci dabobbi ke nishadantar da masu ziyara.

6. Kare Muhalli: Gabon ta yi kaurin suna wajen kare muhalli ta hanyar bai wa tsirrai da hallitu kulawa ta musamman.

7. Yawon Bude Ido: Kasar tana ba da dama don yawon shakatawa da bude ido, wanda baki ke ziyarta don ganin nau’ikan halittu na musamman.

8. Karacin Mutane: Duba da rashin yawan al’ummar kasar, Gabon tana kiyaye daidaito tsakanin ayyukan dan adam da yanayin kasar.

9. Masana’antar Mai: Duk da kasancewarta kasa mai fitar da mai, Gabon ta dauki matakai don rage tasirin muhalli da saka hannun jari kan tsirrai.

10. Kasa Mai Cike Da Al’adun Gargajiya: Kasar na da tarin al’adun gargajiya sannan ta samu ci gaban zamani ta hanyar samun abubuwan more rayuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Wang yi

Ministan Wajen Sin Ya Tayawa Takwaransa Na Najeriya Murnar Kama Aiki Ta Wayar Tarho

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.