ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Gabon 

by Sadiq
3 years ago
Gabon

Gabon, Kasa ce da ke Yammacin gabar tekun Afirka ta Tsakiya, sannan kasa ce da Allah ya albarkace ta da yalwar dazuka da kuma namun daji iri daban-daban, sannan suna da sadaukar da kai don ci gabansu.

Kazalika, Gabon kasa ce da ta ke da burin dorewa a matsayin kasa don samun ci gaba mai dorewa, da nufin kare albarkatun kasa tare da bunkasa tattalin arzikinta.

  • Sojojin Gabon Sun Kama Dan Hambararren Shugaban Kasa Da Laifin Cin Amanar kasa.
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Gabon

Har zuwa safiyar ranar Laraba, Gabon ta kasance karkashin mulkin Shugaba Bongo tun shekarar 1967.

ADVERTISEMENT

Hambararren shugaba Ali Bongo Ondimba ya kasance dan marigayi Omar Bongo, wanda shi ne shugaban kasar Gabon na biyu daga shekarar 1967 har zuwa mutuwarsa a shekarar 2009.

Bayan mutuwar mahaifinsa, Ali Bongo ya lashe zaben shugaban kasar Gabon na 2009, inda ya zama shugaban kasar na uku.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

An sake zabensa a shekarar 2016, a zabukan da aka yi mai cike da cece-kuce na rashin bin ka’ida, take hakkin dan Adam, da zanga-zangar bayan zabe da tashin hankali.

An kuma ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben 2023 na Gabon mai cike da cece-kuce. A ranar 30 ga watan Agusta, 2023 ne dakarun sojin Gabon suka yi juyin mulki na biyu a tarihin Gabon tun bayan samun ‘yancin kan kasar a shekarar 1960, inda suka yi juyin mulki na farko a shekarar 1964.

Abubuwa 10 na musamman game da Gabon:

1. Yalwar Dazuka: Gabon tana alfahari da yawan dazuka a kasar, wanda hakan ke taimaka mata wajen bunkasa tattalin arzikinta.

2. Mayar Da Hankali Kan Ci Gaba: Ƙasar ta himmatu wajen samar da ci gaba mai dorewa, ta hanyar kebe wani yanki mai yawa na kasart matsayin wuraren shakatawa kamar irin su Loango National Park, wanda ke ba da kariya ga namun daji da sauran wuraren shakatawa da ke bakin teku.

3. Bambance-bambancen Al’adu: Gabon kasa ce mai kabilu sama da 40, kowannensu yana da al’adunsa da harsuna daban-daban.

4. Manyan Namun Daji: Kasa mai tarin manyan namun daji kamar irin su giwaye, gwaggon biri, macizai da sauransu.

5. Wuraren Shakatawa: Wannan ya kunshi muhimman wuraren shakatawa da masu yawon bude ido ke zuwa wanda yawanci dabobbi ke nishadantar da masu ziyara.

6. Kare Muhalli: Gabon ta yi kaurin suna wajen kare muhalli ta hanyar bai wa tsirrai da hallitu kulawa ta musamman.

7. Yawon Bude Ido: Kasar tana ba da dama don yawon shakatawa da bude ido, wanda baki ke ziyarta don ganin nau’ikan halittu na musamman.

8. Karacin Mutane: Duba da rashin yawan al’ummar kasar, Gabon tana kiyaye daidaito tsakanin ayyukan dan adam da yanayin kasar.

9. Masana’antar Mai: Duk da kasancewarta kasa mai fitar da mai, Gabon ta dauki matakai don rage tasirin muhalli da saka hannun jari kan tsirrai.

10. Kasa Mai Cike Da Al’adun Gargajiya: Kasar na da tarin al’adun gargajiya sannan ta samu ci gaban zamani ta hanyar samun abubuwan more rayuwa.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Wang yi

Ministan Wajen Sin Ya Tayawa Takwaransa Na Najeriya Murnar Kama Aiki Ta Wayar Tarho

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.