• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
APC

Jam’iyyar APC mai mulki ta dage taronta na kwamitin koli na kasa da na kwamitin zartarwa na kasa har zuwa wani lokaci.

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranakun 11 da 12 ga watan Satumba domin gudanar da tarukan kwamitoci guda biyu, biyo bayan amincewar da Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Kasashen Duniya Wajen Sa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mutane Masu Bukata Ta Musamman
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutum 49 A Yankuna 226 A Kano — SEMA

Jam’iyyar ta kuma umurci mambobin kwamitocin guda biyu da su halarci taron.

Sai dai sakataren yada labaran jam’iyyar APC na asa, Barista Felid Morka ya sanar da dage taron biyu a wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Litinin.

Sanarwar ta ce, “Ana sanar da mambobin kwamitin koli da na kwamitin zartarwa na kasa na jam’iyyar APC cewa, tarukan da aka shirya gudanarwa a ranakun 11 da 12 ga Satumba, 2024, an dage su har zuwa wani lokaci.”

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Jam’iyyar ba ta bayyana dalilan da ya sa ta dage tarukan ba, amma ana ganin cewa jam’iyyar ta dauki wannan mataki ne saboda shugaban kasa baya nan.

Babban sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Basiru, ya bayyana cewa jam’iyyar APC za ta gudanar da babban tarukan ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sakataren ya ce tarukan za su duba halin da jam’iyyar ke ciki da samar da hanyoyin magance kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta da zayyana wasu dabaru da za a aiwatarwa domin samun nasarar jam’iyyar.

Kwamitin koli na kasa na jam’iyyar APC ya kunshi dattawa da wasu daga cikin manyan jami’ai da shugabannin majalisa da masu mataimaka wa jam’iyyar wajen cimma matsaya kan batutuwan da za a tattauna a taron kwamitin zartarwa.

Haka kuma kwamitin na bayar da shawara ga jam’iyya da shugaban kasa.

Ana sa ran Shugaban Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima za su halarci tarukan.

Sauran wadanda ake sa ran za su halarci tarukan sun hada da manyan mambobin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC (NWC), karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Ganduje, tsohon shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa wadanda ’yan jam’iyya ne, manyan jami’ai na majalisar dokokin kasa na da da na yanzu, da tsaffin shugabannin jam’iyyar na kasa da sakatarorin jam’iyyar da jiga-jigan jam’iyyar guda biyu kowanne daga sassar kasar nan.

Basiru ya ce taron zai yi la’akari da rahoton binciken kudi na shekarar 2023/2024 tare da amincewa da kasafin kudin jam’iyyar na shekara mai zuwa.

Ya ce wani muhimmin abu a cikin ajandar taron shi ne, sake duba rajistar jam’iyyar APC, wanda ake sa ran zai kara kaimi ga mambobin jam’iyyar da kuma samar da sahihin bayanai game da adadin mambobin jam’iyyar a fadin kasar.

Ya kara da cewa, gabanin tarukan, jam’iyyar ta kaddamar da cibiyar ci gabanta a wani bangare na kokarin da take yi na gyara akidarta da kuma bayar da horo ga ‘ya’yan jam’iyyarta.

Basiru ya ce, “Taron zai kayyade ranar da za a gudanar da babban taron da ba na zabe ba. Babban taron kasa shi ne mafi girman tsarin yanke shawara na jam’iyyar. Muna da nau’i biyu na al’ada. Na farko shi ne, taron zabe. Bayan haka, muna kuma da babban taron tsakiyar wa’adi, wanda ba zababbu ba ne. Shugabannin jam’iyyar ne za su yanke hukunci kan haka.

“Tarukan za su sake duba zabukan da suka gabata da kuma da tsara yadda za a gudanar da zabukan Edo da Ondo, wanda za a yi a wannan watan da Nuwamba.”

Basiru ya ce bai san da rade-radin da ake yi cewa taron kwamitin zartarwa zai tantance makomar wasu jami’an jam’iyyar ba.

“Duk wani abu da ba a cikin ajandar tarukan ba mu sanan shi ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

'Yansanda sun Kama Masu Laifi 26, Sun Kwato Wayoyin Sata 126 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.