• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Abubuwan Da Ake Sa Ran APC Ta Tattauna A Taron Kwamitin Zartarwarta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC mai mulki ta dage taronta na kwamitin koli na kasa da na kwamitin zartarwa na kasa har zuwa wani lokaci.

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranakun 11 da 12 ga watan Satumba domin gudanar da tarukan kwamitoci guda biyu, biyo bayan amincewar da Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi.

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Aiki Tare Da Kasashen Duniya Wajen Sa Kaimi Ga Raya Sha’anin Mutane Masu Bukata Ta Musamman
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutum 49 A Yankuna 226 A Kano — SEMA

Jam’iyyar ta kuma umurci mambobin kwamitocin guda biyu da su halarci taron.

Sai dai sakataren yada labaran jam’iyyar APC na asa, Barista Felid Morka ya sanar da dage taron biyu a wata sanarwa da ya fitar a daren ranar Litinin.

Sanarwar ta ce, “Ana sanar da mambobin kwamitin koli da na kwamitin zartarwa na kasa na jam’iyyar APC cewa, tarukan da aka shirya gudanarwa a ranakun 11 da 12 ga Satumba, 2024, an dage su har zuwa wani lokaci.”

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Jam’iyyar ba ta bayyana dalilan da ya sa ta dage tarukan ba, amma ana ganin cewa jam’iyyar ta dauki wannan mataki ne saboda shugaban kasa baya nan.

Babban sakataren jam’iyyar APC na kasa, Sanata Ajibola Basiru, ya bayyana cewa jam’iyyar APC za ta gudanar da babban tarukan ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sakataren ya ce tarukan za su duba halin da jam’iyyar ke ciki da samar da hanyoyin magance kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta da zayyana wasu dabaru da za a aiwatarwa domin samun nasarar jam’iyyar.

Kwamitin koli na kasa na jam’iyyar APC ya kunshi dattawa da wasu daga cikin manyan jami’ai da shugabannin majalisa da masu mataimaka wa jam’iyyar wajen cimma matsaya kan batutuwan da za a tattauna a taron kwamitin zartarwa.

Haka kuma kwamitin na bayar da shawara ga jam’iyya da shugaban kasa.

Ana sa ran Shugaban Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima za su halarci tarukan.

Sauran wadanda ake sa ran za su halarci tarukan sun hada da manyan mambobin kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar APC (NWC), karkashin jagorancin Dakta Abdullahi Ganduje, tsohon shugaban kasa da mataimakin shugaban kasa wadanda ’yan jam’iyya ne, manyan jami’ai na majalisar dokokin kasa na da da na yanzu, da tsaffin shugabannin jam’iyyar na kasa da sakatarorin jam’iyyar da jiga-jigan jam’iyyar guda biyu kowanne daga sassar kasar nan.

Basiru ya ce taron zai yi la’akari da rahoton binciken kudi na shekarar 2023/2024 tare da amincewa da kasafin kudin jam’iyyar na shekara mai zuwa.

Ya ce wani muhimmin abu a cikin ajandar taron shi ne, sake duba rajistar jam’iyyar APC, wanda ake sa ran zai kara kaimi ga mambobin jam’iyyar da kuma samar da sahihin bayanai game da adadin mambobin jam’iyyar a fadin kasar.

Ya kara da cewa, gabanin tarukan, jam’iyyar ta kaddamar da cibiyar ci gabanta a wani bangare na kokarin da take yi na gyara akidarta da kuma bayar da horo ga ‘ya’yan jam’iyyarta.

Basiru ya ce, “Taron zai kayyade ranar da za a gudanar da babban taron da ba na zabe ba. Babban taron kasa shi ne mafi girman tsarin yanke shawara na jam’iyyar. Muna da nau’i biyu na al’ada. Na farko shi ne, taron zabe. Bayan haka, muna kuma da babban taron tsakiyar wa’adi, wanda ba zababbu ba ne. Shugabannin jam’iyyar ne za su yanke hukunci kan haka.

“Tarukan za su sake duba zabukan da suka gabata da kuma da tsara yadda za a gudanar da zabukan Edo da Ondo, wanda za a yi a wannan watan da Nuwamba.”

Basiru ya ce bai san da rade-radin da ake yi cewa taron kwamitin zartarwa zai tantance makomar wasu jami’an jam’iyyar ba.

“Duk wani abu da ba a cikin ajandar tarukan ba mu sanan shi ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKwamitiTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Binciken Badakalar Mai

Next Post

‘Yansanda sun Kama Masu Laifi 26, Sun Kwato Wayoyin Sata 126 A Kano

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

'Yansanda sun Kama Masu Laifi 26, Sun Kwato Wayoyin Sata 126 A Kano

LABARAI MASU NASABA

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.