ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutum 49 A Yankuna 226 A Kano — SEMA

by Sadiq
2 years ago
Ambaliyar Ruwa

Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa ta Jihar Kano (SEMA), ta tabbatar da mutuwar mutane 49 a yankuna 226 sakamakon ambaliyar ruwa da iska mai karfi a kananan hukumomi 27 tun daga watan Janairu 2024.

Sakataren Hukumar, Isyaku Abdullahi Kubarachi ne, ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a Kano a ranar Laraba.

  • Hasashen Ambaliya: Gwamna Nasir Ya Kafa Kwamitin Daukar Matakin Gaggawa A Kebbi
  • Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Miyagun Kwayoyi A Kano

Ya bayyana cewa Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMET), ta yi hasashen ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 14, amma Iftila’in ya shafi wurare fiye da haka.

ADVERTISEMENT

Ya ce yankunan da abin ya shafa da sun hada da Tudun Wada, Gwale, Wudil, Danbatta, Ajingi, Dala, Gwarzo, Madobi, Bichi, Kano Municipal, Karaye, Tarauni, Minjibir, Bebeji, Rogo, Shanono, Kabo, Garin Malam, da Ungogo.

Sauran sun hada da Kumbotso, Nassarawa, Kura, Dawakin Kudu, Dawakin Tofa, Gezawa, Rogo da Bagwai.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

“Ambaliyar ta lalata gidaje 6,583 tare da shafar mutum 38,814 a fadin jihar. Kazalika, gonaki 8,289 da ke da fadin eka 36,265 sun lalace. Iftila’in ya tilasta wa mutum 1,414 yin hijira, ya jikkata 139, kuma ya kashe mutum 49,” in ji Kubarachi.

SEMA tare da hadin gwiwar wasu hukumomi sun raba kayan agaji domin rage radadi ga wadanda abin ya shafa.

Hukumar ta kuma shirya tarukan bita don hana afkuwar irin wannan Iftila’i a gaba.

Kubarachi, ya gode wa Gwamna Abba Yusuf bisa goyon bayansa ta wajen samar da kayan aiki da sauran abubuwan da suka taimaka wajen daukar matakin gaggawa.

Ya yi gargadi ga al’ummar jihar da su guji gine-gine a kan magudanan ruwa kuma su tabbatar da tsaftace magudanan don rage hatsarin ambaliyar ruwa.

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwan Maiduguri Ta Shafi Mutane Sama Da Miliyan 1 – Gwamnati

Ambaliyar Ruwan Maiduguri Ta Shafi Mutane Sama Da Miliyan 1 - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.