• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina

by Zaharadden Umar
7 days ago
in Manyan Labarai
0
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Sulhu Da Ƴan Bindiga A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙaramar Hukumar Faskari a jihar Katsina ta bi sahun sauran ƙananan hukumomi wajen shirya taron zaman sulhu da ɓarayin daji domin samun zaman lafiya a wannan yanki.

Ita dai ƙaramar hukumar Faskari ita ce ta takwas da ta shiga wannan yarjejeniyar zaman lafiya da ɓarayin daji gwamnatin jihar Katsina ke cewa ba ruwan ta, amma dai zata dauki mataki akan duk wanda ya karya Yarjejeniyar.

Wannan zaman sulhu ya ɗauki hankali fiye da kowane musamman ganin wasu fuskokin manyan ɓarayin daji da suka halarci taron wanda masana ke cewa lallai a sanya hankali da tunani wajen yin wannan yarjejeniya.

Daga cikin waɗanda aka ga fuskokin su akwai irin su Ado Aleiro ƴ an kuza da Kachalla Isiya Akwashi Garwa da Babaro wanda ake zargin ya jagoranci kisan massalata fiye da 30 a garin gidan Mantau a watan da ya gabata shine ya halarci taron.

  • ’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa
  • Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Shi dai wannan taron an gudanar da shi a ranar lahadin da ta gabata 14 ga watan Satumba, 2025 a garin Hayin Gada Bilbis bisa waru sharuɗa da aka gindaya.

Labarai Masu Nasaba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

A ɓangaren al’umma an samu halartar shugaban ƙaramar hukumar Faskari Hon. Surajo Aliyu Daudawa da Ɗan Majalisa dokokin mai wakiltar ƙaramar hukumar Faskari injiniya Sama’ila Mu’azu Bawa.

Sauran sun haɗa da Hakimin Faskari da kuma na Mai Ruwa da wakilan al’umma da masu riƙe da masarautar gargajiya da sauran al’umma.

Sai kuma ɓangaren ɓarayin daji inda aka samu halartar manyan jiga-jigan da suka kwarai wajen tada zaune tsaye a yankin Funtua baƙi ɗaya.

Mutane iri su Ado Aleiro Ƴan Kuza da Kachalla Hassan Sarkin Fulani Mai Taru da Kachalla Isiya Akwashi Garwa  da Kachalla Sari da kuma Alhaji Abdullahi da sauran dakarun daji duk sun halarci wannan zaman sulhu.

Rahotanni sun bayyana cewa an cimma wasu sharuɗa kafin a kulla wannan yarjejeniya tsakanin al’ummar ƙaramar hukumar Faskari da kuma su shugabannin ƴ an bindiga kamar haka;

Su Fulani ko ɓarayin daji su daina kashe kowa ko sace jama’a domin yin garkuwa da su a nemi kuɗin fansa a ƙaramar hukumar Faskari

Sannan su Fulani sun amince kowa ya shiga daji ya yi aikin gona da kuma masu saran itacce ko zuwa zumunci a duk inda suke so an amince da haka sannan za su sako waɗanda suka yi garkuwa da su.

Suma a ɓangaen wakilan al’umma sun gindaya cewa an amince ɓarayin daji su shiga ko’ina a ƙaramar hukumar Faskari kamar yadda aba ake yi, amma ba tare da bindiga ko wani makami ba.

Kazalika an amincewa ɓarayin daji su ziyarci asibitoci domin duba lafiyar su ba tare da an tsangwame su ba, sannan su mayar da yaran su makarantar Boko

Abu na ƙarshe a cikin yarjejeniyar shi ne, an amincewa ɓarayin daji su cigaba da mu’amularsu ta yau da kullum kamar cin kasuwa, saye da sayarwa kamar kowa ba tare da wata fargaba ba.

Al’ummar da wannan iftila’i ya shafa sun amince da wannan yarjejeniya wanda suka ce ita ce hanya guda ɗaya da ta rage masu domin su zauna lafiya su da iyalansu.

Wasu kuma na sukar wannan sasanci da cewa to yanzu ina makomar waɗanda aka zalunta aka kashe masu ƴ an uwa da ɓarnata masu dukiyoyi? Suma a bangaren ɓarayin daji sun koka da irin ɓarnar da aka yi masu.

Fatan da ake da shi yanzu shine idan haka zai zama maslaha tsakanin al’umma da kuma ɓarayin daji to Allah ya tabbatar da ɗorewar lamarin a jihar Katsina da arewacin Nijeriya baƙi ɗaya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyBanditKatsinaPoliceSulhu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ɗantsoho Ya Mayar Da Hankali Wajen Farafaɗo Da Martaba Da Ƙimar NPA

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Related

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba
Manyan Labarai

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

10 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas
Manyan Labarai

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

12 hours ago
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa
Manyan Labarai

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

13 hours ago
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

14 hours ago
Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

23 hours ago
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

1 day ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

Gwamnatin Tarayya Na Yunƙurin Kawar Da Shanu Daga Titunan Abuja

LABARAI MASU NASABA

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

September 26, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

September 26, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

September 26, 2025
An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

September 26, 2025
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

September 26, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.