• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna

by Shehu Yahaya and Sulaiman
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Yadda Abin Ya Faru –Ganau
  • Tabbas ‘Yan Ta’adda Muka Farmaka –NAF

Al’ummar Kauyen Jika da Kolo da ke garin Yadin Kidandan a karamar hukumar Giwa da ke Jihar Kaduna na ci gaba da zaman dar-dar bisa zargin kai musu hari da jiragen sojin saman Nijeriya ya kai musu a makon da ya gabata.

 

Al’ummar garin sun zargi sojojin sama da jefa musu bam yayin da suke gudanar da sallar Juma’a a cikin masallaci da kuma kasuwa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 23.

  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Za Su Kaɗa Ƙuri’ar Kawo Canji Na Gaskiya A 2027 – Kwankwaso
  • Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

Harin bam din ya haifar da cece-kuce tsakanin al’ummar garin da runduna sojin saman Nijeriya, inda mutanan kauyen suke zargin sojoji sun kai harin mai uwa da wabi.

 

Labarai Masu Nasaba

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

Sai dai a nata, bangaren rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta wanna zargi, ta kuma bayyana cewa harin da ta kai ya tafi kai tsaye ne ga sansanin babban dan bindiga mai suna Kadade Gurgu, wanda na hannun daman dan ta’adda Dogo Gide ne.

 

A wata ziyara da wakilinmu ya kai a yankin karamar hukumar Giwa, wasu mazauna garin sun bayyana cewa akwai fararen hula da harin sojojin ya shafa.

 

Haka zalika, sun kamanta harin da sojojin suka kai da wanda aka kai a baya a garin Tudun Biri, wanda ya yi sanadiyyar rasa ran masu Mauludi kimamnin guda 100 a watan Disamban 2023.

 

Wani magidancin dan asalin garin Kidandan, ya bayyana wa wakilinmu yadda abin ya faru, yana mai cewa, “Bisa batun tsaro ba zan iya bayyana sunana ba, amma dai ni dan asalin garin Kidandan ne kuma a nan aka haife, sannan a nan nake rayuwa, bisa matsalar tsaro ya sanya muke zuwa garin jifa-jifa.

 

“Yadin Kidandan gari ne wanda ya zama sansanin ‘yan ta’adda. Wanda yanzu shiga garin idan kai ba dan gari ba ne ba ya shiguwa. Ranar Juma’ar da ta gabata, wani jirgi ya kai hari har ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Amma batun gaskiya shi ne, har yanzu babu wani wanda zai iya tantance cewa wadanda suka mutu a harin ‘yan garin ne kadai babu ‘yan ta’adda a ciki, saboda gari ne wanda yake cakude da mutanan kirki da ‘yan ta’adda.”

 

Wani mazaunin garin Jika da Kolo da ke zaune a garin Gwargwaji a Zariya ya shaida cewa, “Yawancinmu har yanzu muna zaune a kusa da kauyen, saboda ba mu da wani wurin da za mu koma. A nan aka haifi kakanninmu.

 

Mun rasa ‘yan uwanmu da yawa, ciki har da yara marasa laifi.

 

“Kuma batun cewa harin ya rusa da masallaci ba haka ba ba ne. An dai kashe mutane amma harin bai taba masallaci ba.”

 

Sai dai wani bincike da LEADERSHIP HAUSA ta gudanar ya nuna cewa masallacin da al’ummar garin na Jika da Kolo suke zargin sajojin sun kai hari, dan siyasa daga Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali Amin “Little”, ya gina musu. Wanda yake kusa da wat babbar gonarsa da ke yankin domin gudanar da sallar Juma’a.

 

Majiyarmu ta shaida mana cewa shekaru biyu baya, shi kansa dan siyasar ya tsallake rijiya da baya daga hannun ‘yan ta’adda, inda aka harbe shi a hannu, lamarin da sanya ya dakatar da zuwa gonar bisa matsalar rashin tsaro.

 

A wata sanarwar da rundunar sojan sama ta fitar ta hannun daraktan yada labaranta, Kaftin Kabiru Ali, ya jaddada cewa ba su Kai hari a masallaci ba, kuma duk wani bayani zai zo ne bayan da rundunar ta kammala bincike.

 

Rundunar ta kara da cewa ta kashe ‘yan ta’adda da dama yayin harin da ta kai, amma babu masallaci a wurin da jiragen suka kai harin.

 

A wata zantawa da ya yi da wakilinmu, Kansilar Mazabar Kidandan, Abdullahi Ismail, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce kauyen Jika da Kolo ya zama sansanin ‘yan ta’adda da suke cin kasuwarsu babu babbaka.

 

Majiyarmu ta tabbatar da cewa an yi jana’izar mutane da suka ransu su 23.

 

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin kwamshinan harkokin tsaro na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan kan lamarin, inda ya kira wayarsa har sau uku bai dauka ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'ummar Tudun BiriHarin sojoji ga yan gariNAF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Za Su Kaɗa Ƙuri’ar Kawo Canji Na Gaskiya A 2027 – Kwankwaso

Next Post

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Related

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

2 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

3 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

7 hours ago
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

15 hours ago
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
Manyan Labarai

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

16 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

24 hours ago
Next Post
NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

August 12, 2025
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

August 12, 2025
’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

’Yan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 6 A Taraba

August 12, 2025
Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

August 12, 2025
Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

Ba Iya Yunwa Ce Kaɗai Ke Kashe Ƙananan Yara A Katsina Ba – Gwamnati

August 12, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

August 12, 2025
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.