ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Nijeriya

Aikin gina bututun gas tsakanin Nijeriya da Morocco ya kai wani sabon mataki bayan tarukan kwamitin fasaha da na jagoranci da aka gudanar a Rabat, babban birnin Morocco. Wannan gagarumin aiki wanda zai ratsa ƙasashe 13 na Afrika, an tsara shi ne domin isar da iskar gas daga Nijeriya zuwa Turai ta bakin tekun yammacin Afrika, tare da amfanar ƙasashen da bututun zai ratsa.

Sanarwar da Hukumar Harkokin Ma’adanai da Man Fetur ta Morocco (ONHYM) ta fitar ta bayyana cewa an kammala binciken fasaha da na tasirin muhalli a sashin arewa na bututun, yayin da ake ci gaba da irin wannan bincike a sashin kudu daga Nijeriya zuwa Senegal. Har ila yau, an kafa kamfanin da zai jagoranci aikin (Holding Company), tare da ƙirƙirar ƙananan kamfanoni (SPVs) don kula da kowane sashi na aikin.

  • Hukumar CAF Ta Sanar Da Garuruwan Da Za A Buga Gasar AFCON 2025 A Morocco
  • Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

A lokacin taron da aka gudanar a Rabat a ranar 10 da 11 ga Yuli, kamfanonin NNPC daga Nijeriya, ONHYM daga Morocco da SOTOGAZ daga Togo sun rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniya, wacce ta tabbatar da aikin shiga Togo cikin. Wannan mataki ya kammala haɗin gwuiwa tsakanin dukkan ƙasashen da bututun zai ratsa.

ADVERTISEMENT

Bututun zai fara daga Nijeriya, ya wuce ta ƙasashen Benin, Togo, Ghana, Côte d’Ivoire, Liberia, Sierra Leone, Guinea, Guinea-Bissau, Gambia, Senegal, da Mauritania kafin ya isa Morocco. Daga nan kuma, zai haɗu da bututun Maghreb-Europe da hanyoyin iskar gas na Turai, tare da samar da gas ga ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso.

Wannan aikin, wanda aka fara ƙarƙashin jagorancin Sarkin Morocco Mohammed VI da Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, yana da nufin ƙarfafa haɗin kai, tattalin arziƙi, da ci gaban ƙasashen Afrika. Ana sa ran aikin zai zama jigo wajen inganta rayuwar al’ummomi, da haɓaka amfani da makamashi mai tsafta, da ƙarfafa haɗin gwuiwar yankin Atlantic.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Ba Zamu Dawo Da Sanata Natasha Zauren Majalisa Ba, Sai Mun Karɓi Kwafin Hukuncin Kotu - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.