• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akalla Malamai 100 Daga Arewacin Nijeriya Suka Yi Addu’ar Samun Nasarar Zaben 2023

by Sulaiman and Shehu Yahaya
3 years ago
Zabe

Ayayin da ake shirin bikin ranar zaman lafiya da addu’a ta duniya na ranar 21 ga watan Yuni 2022, akalla malamai dari (100) da suka hada da musulmi da kiristoci daga jihohin arewacin Nijeriya ne suka hadu, yayin da wasu suka gabatar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da hadin kai a wuraren ibadarsu da ya gudana a Jihar Kaduna.

Malaman sun bayyana cewa Allah ya nufe su ne da su yi magana a madadin wadanda ba za su iya yin magana da kansu domin bukatar dorewar zaman lafiya, fahimtar juna, hakuri da afuwa a tsakanin kungiyoyi addinai daban-daban.

  • 2023: INEC Ta Kafa Sharuda Biyu Ga jam’iyyun Da Ke Son Sauya Abokan Takara

Da yake bayani babban mai kula da cocin ‘Christ Evangelical and life intervention ministry’, Fasto Yohanna Buru, ya bayyana cewa akwai bukatar yin hakan ranar bikin wannan shekara na zaman lafiya da addu’o’i ta duniya.

A cewarsa, kungiyar fastoci da ‘yan’uwa a fadin kasar nan wadanda suka hada da kungiyarsa ta (Peace Revival and Recounciliation Foundation of Nigeria) na da bukatar a fara gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar domin babban zabe na 2023 mai zuwa.

Ya ce a daidai lokacin da babban zaben shekarar 2023 ke gabatowa, dukkan masu neman kujerar sanata, gwamna da shugaban kasa na bukatar addu’o’in neman tsarin Allah da nasara, don haka akwai bukatar dukkanin malaman addini su shirya addu’a ga ‘yan takara ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasarsu ba.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Ya ce “Muna addu’ar Allah ya ba su hikima ta yadda za su wakilci kowa a kasar nan ba tare da la’akari da al’adu, addini, yanki, da dai sauransu ba”
“Ya Ubangiji, ka ba shugabanninmu hikima domin su yi abin da ya fi karfin fahimtarsu.

Ka taimakesu su zabi hanyar da ta dace a lokacin da suke yanke shawara a madadin wannan al’umma.”
Da yake mayar da jawabi, Malam Mohammed Sani, daya daga cikin Malaman addinin Musulunci na Kaduna ya yi kira ga Musulmi da Kirista da su rika yi wa shugabansu addu’a.

Ya kara da cewa yana da kyau kowane dan kasa ya rika mara wa shugabansa baya da addu’o’i masu kyau, domin Allah ya taimake shi ya sauke nauyin da yake kansa.

Daga nan sai ya yi kira ga ‘yan siyasa da su daina amfani da ‘yan daba a lokacin yakin neman zabe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.