• Leadership Hausa
Thursday, September 28, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa yadda lamura suke gudana a halin yanzu, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), tana bukatar samun cikakken goyon baya daga wurin masu ruwa da tsaki kafin ta samu hanyar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Shekaru da dama ‘yan siyasan Nijeriya suna kokarin bin duk wata hanya domin zama kan karagar mulki tare da amfani da ofishinsu wajen ci gaba da mulkar al’umma.

  • INEC Ta Tabbatar Da Cafke Jami’inta Da Ke Karbar Na Goro Yana Wa Jama’a Rijistar Zabe A Ribas

Sahihin zabe kuma karbabbe ga mutane ya kasance yana da tushe da ke rike da dimokuradiyya a ko’ina a fadin duniya. Sai dai abun takaici a Nijeriya wadannan ginshikai na dimokuradiyya suna nema su zama tarihi.

Rashin tsari da amfani da kudade da akidar jari hujja da rabuwar kawuna da kuma kokarin ci gaba da zama a kan karagar mulki sun jefa siyasar Nijeriya cikin rashin tabbas wanda ‘yan siyasa a Nijeriya suke amfani da su a matsayin makamin zama a kan mulki.

Lallai wadannan rashin tsari a cikin siyasar Nijeriya ba za su iya samar da kyakkyawan gwamnati ba ballantana a samu bunkasan tattalin arziki a cikin kasar nan, domin suna iya zama wani bakan gizo ne da zai iya hadiye ayyukan gwamnatin da za ta hau karagar mulki na tsawan shekaru 10. Alal misali, kamar yadda ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC suka biya kudin tikitin takara na naira miliyan 100 da kuma ‘yan takarar shugaban kasa karkashin PDP da suka sayi tikitin takara a kan naira miliyan 40.

Labarai Masu Nasaba

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

Akwai abun mamaki a kan haka, ganin yadda mafi yawancin ‘yan Nijeriya da suke fama da yunwa, wanda wadannan kudade zai iya ciyar da su ko da na wata daya ne.

Babban abin takaicin ma dai shi ne, yadda ‘yan siyasa masu neman takara suke raba wa daliget daloli domin su zabe su a lokacin zaben fid da gwani da suka gabata.

Don haka, idan aka duba irin wadannan abubuwa a cikin siyasar Nijeriya akwai abin damuwa a kan ko INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe a 2023?.
Idan har ‘yan siyasa za su ci gaba da gudanar da irin wadannan mugayen dabi’u a cikin siyasar Nijeriya, to ta yaya za a iya samun sahihin zabe. Idan har wanda ya ci zabe ba ta hanyar da ya inganta ba, zai kasance manufofinsa da tsare-tsarensa ba za su iya bunkasa tattalin arzikin kasar nan ba.

Wajibe ne sahihin zabe ya kasance wanda mutane suke zabe shi ya samu nasara, a nan dole ne INEC ta ci gaba da samun goyon bayan masu ruwa da tsaki domin samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Idan aka duba irin matsalolin da kasar nan take fuskanta, zaben 2023 zai kasance mai matukar cike da kalubale ga hukumar INEC.

Miliyoyin ‘yan Nijeriya suna nuna halin ko-in-kula game da zabe sakamakon cewa ko sun jefa kuri’a ba a amfani da ita wajen fitar da sakamakon zabe. Domin haka, sun gunmaci amsar kudade daga hannun ‘yan siyasa kafin su jefa kuri’arsu.
Wasu ‘yan siyasa suna amfani da yakin neman zabe wajen tayar da zaune-tsaye da zai iya kawo hargitsi wanda ke shafar gudanar da sahihin zabe, to dole ne hukumar INEC da dauki mataki a kan haka.

Hakazalika, ko a zaben Jihar Ekiti da gudana sai da jam’iyyar PDP ta yi korafin cewa, APC ta yi amfani da kudi wajen lashe zabe a jihar.

Hukumar INEC ta bayyana sunan dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC, Abiodun Oyebanji a matsayin wanda ya lashe zaben Jihar Ekiti da ya gudana a ranar Asabar da ta gabata.

Shi dai Oyebanji ya samu nasara ne a kananan hukumoni 15 cikin 16 da ke fadin jihar, inda ya samu kuri’u guda 187,057. Yayin da dan takarar da ke binsa, Segun Oni ya samu kuri’u 82,211, sai kuma dan takarar jam’iyyar PDP, Bisi Kolawole ya samu kuri’u 67,457.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akalla Malamai 100 Daga Arewacin Nijeriya Suka Yi Addu’ar Samun Nasarar Zaben 2023

Next Post

Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Related

Akpabio
Tambarin Dimokuradiyya

Munakisar Da Ke Cikin Batun Tsige Akpabio

5 days ago
Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

5 days ago
Kotu
Tambarin Dimokuradiyya

Martanin Da Ya Biyo Bayan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnonin Kano, Bauchi Da Zamfara 

6 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

2 weeks ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

2 weeks ago
Zaben Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Karar Zaben Shugaban Kasa: Ko Ya Za Ta Kaya A Kotun Koli?

2 weeks ago
Next Post
Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Ghana Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Ghana

September 28, 2023
Bamu Da Niyyar Cin Zarafin Victor Osimhen-Napol

Bamu Da Niyyar Cin Zarafin Victor Osimhen-Napol

September 28, 2023
Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

Adadin Jarin Da Kasar Sin Ta Zuba A Kasashen Waje A Shekarar 2022 Na Kan Gaba A Duniya

September 28, 2023
Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo

Cibiyar Kimiyyar Noma Na Sin CATAS Ta Cancanci Yabo

September 28, 2023
CISA: Masana’antun Sarrafa Karfe Na Tafiya Cikin Yanayi Mai Karko Tsakanin Watan Janairu Zuwa Na Agusta

CISA: Masana’antun Sarrafa Karfe Na Tafiya Cikin Yanayi Mai Karko Tsakanin Watan Janairu Zuwa Na Agusta

September 28, 2023
Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

Gwamna Uba Sani Ya Taya Kansa Murna Da Hukuncin Da Kotun Zaben Kaduna Ta Yanke

September 28, 2023
Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tsunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

Babu Wata Yarjejeniya Tsakaninmu Da Gwamnatin Tarayya Kan Dakatar Da Yajin Aiki – NLC

September 28, 2023
Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

Masana Kimiyya Na Sin Da Afrika Sun Lashi Takobin Hada Gwiwa Wajen Ganin An Cimma Ajandar Kyautata Rayuwar Jama’a

September 28, 2023
“Wasannin Asiya Na Zamani” Wata Taga Ce Ta Lura Da Yadda Ake Gudanar Da Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin

“Wasannin Asiya Na Zamani” Wata Taga Ce Ta Lura Da Yadda Ake Gudanar Da Zamanintarwa Irin Na Kasar Sin

September 28, 2023
Xi Ya Yi Kira Da A Samar Da Sabbi Da Manyan Gudummawa Don Ciyar Da Harkokin Mata Da Yara Gaba

Xi Ya Yi Kira Da A Samar Da Sabbi Da Manyan Gudummawa Don Ciyar Da Harkokin Mata Da Yara Gaba

September 28, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.