ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Inec

Bisa yadda lamura suke gudana a halin yanzu, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta Ta Kasa (INEC), tana bukatar samun cikakken goyon baya daga wurin masu ruwa da tsaki kafin ta samu hanyar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Shekaru da dama ‘yan siyasan Nijeriya suna kokarin bin duk wata hanya domin zama kan karagar mulki tare da amfani da ofishinsu wajen ci gaba da mulkar al’umma.

  • INEC Ta Tabbatar Da Cafke Jami’inta Da Ke Karbar Na Goro Yana Wa Jama’a Rijistar Zabe A Ribas

Sahihin zabe kuma karbabbe ga mutane ya kasance yana da tushe da ke rike da dimokuradiyya a ko’ina a fadin duniya. Sai dai abun takaici a Nijeriya wadannan ginshikai na dimokuradiyya suna nema su zama tarihi.

ADVERTISEMENT

Rashin tsari da amfani da kudade da akidar jari hujja da rabuwar kawuna da kuma kokarin ci gaba da zama a kan karagar mulki sun jefa siyasar Nijeriya cikin rashin tabbas wanda ‘yan siyasa a Nijeriya suke amfani da su a matsayin makamin zama a kan mulki.

Lallai wadannan rashin tsari a cikin siyasar Nijeriya ba za su iya samar da kyakkyawan gwamnati ba ballantana a samu bunkasan tattalin arziki a cikin kasar nan, domin suna iya zama wani bakan gizo ne da zai iya hadiye ayyukan gwamnatin da za ta hau karagar mulki na tsawan shekaru 10. Alal misali, kamar yadda ‘yan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar APC suka biya kudin tikitin takara na naira miliyan 100 da kuma ‘yan takarar shugaban kasa karkashin PDP da suka sayi tikitin takara a kan naira miliyan 40.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Akwai abun mamaki a kan haka, ganin yadda mafi yawancin ‘yan Nijeriya da suke fama da yunwa, wanda wadannan kudade zai iya ciyar da su ko da na wata daya ne.

Babban abin takaicin ma dai shi ne, yadda ‘yan siyasa masu neman takara suke raba wa daliget daloli domin su zabe su a lokacin zaben fid da gwani da suka gabata.

Don haka, idan aka duba irin wadannan abubuwa a cikin siyasar Nijeriya akwai abin damuwa a kan ko INEC za ta iya gudanar da sahihin zabe a 2023?.
Idan har ‘yan siyasa za su ci gaba da gudanar da irin wadannan mugayen dabi’u a cikin siyasar Nijeriya, to ta yaya za a iya samun sahihin zabe. Idan har wanda ya ci zabe ba ta hanyar da ya inganta ba, zai kasance manufofinsa da tsare-tsarensa ba za su iya bunkasa tattalin arzikin kasar nan ba.

Wajibe ne sahihin zabe ya kasance wanda mutane suke zabe shi ya samu nasara, a nan dole ne INEC ta ci gaba da samun goyon bayan masu ruwa da tsaki domin samun nasarar gudanar da sahihin zabe a 2023.

Idan aka duba irin matsalolin da kasar nan take fuskanta, zaben 2023 zai kasance mai matukar cike da kalubale ga hukumar INEC.

Miliyoyin ‘yan Nijeriya suna nuna halin ko-in-kula game da zabe sakamakon cewa ko sun jefa kuri’a ba a amfani da ita wajen fitar da sakamakon zabe. Domin haka, sun gunmaci amsar kudade daga hannun ‘yan siyasa kafin su jefa kuri’arsu.
Wasu ‘yan siyasa suna amfani da yakin neman zabe wajen tayar da zaune-tsaye da zai iya kawo hargitsi wanda ke shafar gudanar da sahihin zabe, to dole ne hukumar INEC da dauki mataki a kan haka.

Hakazalika, ko a zaben Jihar Ekiti da gudana sai da jam’iyyar PDP ta yi korafin cewa, APC ta yi amfani da kudi wajen lashe zabe a jihar.

Hukumar INEC ta bayyana sunan dan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC, Abiodun Oyebanji a matsayin wanda ya lashe zaben Jihar Ekiti da ya gudana a ranar Asabar da ta gabata.

Shi dai Oyebanji ya samu nasara ne a kananan hukumoni 15 cikin 16 da ke fadin jihar, inda ya samu kuri’u guda 187,057. Yayin da dan takarar da ke binsa, Segun Oni ya samu kuri’u 82,211, sai kuma dan takarar jam’iyyar PDP, Bisi Kolawole ya samu kuri’u 67,457.

Inec
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

Yadda Matafiya 18 Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Hadarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.