ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akalla Malamai 100 Daga Arewacin Nijeriya Suka Yi Addu’ar Samun Nasarar Zaben 2023

by Sulaiman and Shehu Yahaya
4 years ago
Zabe

Ayayin da ake shirin bikin ranar zaman lafiya da addu’a ta duniya na ranar 21 ga watan Yuni 2022, akalla malamai dari (100) da suka hada da musulmi da kiristoci daga jihohin arewacin Nijeriya ne suka hadu, yayin da wasu suka gabatar da addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya da hadin kai a wuraren ibadarsu da ya gudana a Jihar Kaduna.

Malaman sun bayyana cewa Allah ya nufe su ne da su yi magana a madadin wadanda ba za su iya yin magana da kansu domin bukatar dorewar zaman lafiya, fahimtar juna, hakuri da afuwa a tsakanin kungiyoyi addinai daban-daban.

  • 2023: INEC Ta Kafa Sharuda Biyu Ga jam’iyyun Da Ke Son Sauya Abokan Takara

Da yake bayani babban mai kula da cocin ‘Christ Evangelical and life intervention ministry’, Fasto Yohanna Buru, ya bayyana cewa akwai bukatar yin hakan ranar bikin wannan shekara na zaman lafiya da addu’o’i ta duniya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, kungiyar fastoci da ‘yan’uwa a fadin kasar nan wadanda suka hada da kungiyarsa ta (Peace Revival and Recounciliation Foundation of Nigeria) na da bukatar a fara gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar domin babban zabe na 2023 mai zuwa.

Ya ce a daidai lokacin da babban zaben shekarar 2023 ke gabatowa, dukkan masu neman kujerar sanata, gwamna da shugaban kasa na bukatar addu’o’in neman tsarin Allah da nasara, don haka akwai bukatar dukkanin malaman addini su shirya addu’a ga ‘yan takara ba tare da la’akari da jam’iyyun siyasarsu ba.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Ya ce “Muna addu’ar Allah ya ba su hikima ta yadda za su wakilci kowa a kasar nan ba tare da la’akari da al’adu, addini, yanki, da dai sauransu ba”
“Ya Ubangiji, ka ba shugabanninmu hikima domin su yi abin da ya fi karfin fahimtarsu.

Ka taimakesu su zabi hanyar da ta dace a lokacin da suke yanke shawara a madadin wannan al’umma.”
Da yake mayar da jawabi, Malam Mohammed Sani, daya daga cikin Malaman addinin Musulunci na Kaduna ya yi kira ga Musulmi da Kirista da su rika yi wa shugabansu addu’a.

Ya kara da cewa yana da kyau kowane dan kasa ya rika mara wa shugabansa baya da addu’o’i masu kyau, domin Allah ya taimake shi ya sauke nauyin da yake kansa.

Daga nan sai ya yi kira ga ‘yan siyasa da su daina amfani da ‘yan daba a lokacin yakin neman zabe.

Zabe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Zabe
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

Sharhi: Ko INEC Za Ta Samu Nasarar Sahihin Zabe A 2023?

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.