• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ya tabbatar da cewa akwai wadataccen mai da zai ishi ‘yan kasa na kimanin kwanaki 30 duk da cewa an fara ganin dogayen layukan mai tun da maraicen ranar Litinin.

Kungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (IPMAN), ta ce tabbas an fara ganin dogayen layukan mai kuma hakan baya rasa nasaba da furucin shugaba Tinubu amma sai mambobinta sun sayo mai daga NNPCL din a yau kafin ta iya magana a kan batun karin farashin da za a iya gani, lamarin da ya fara sanya fargaba a zukatan ‘yan Nijeriya.

  • Daga Karshe Dai, Cire Tallafin Mai Ya Tabbata, NNPC Na Sayar Da Lita N537 A Abuja
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

Jim kadan bayan ayyana janye tallafin man fetur da sabon shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi a jawabinsa bayan rantsar da shi ne, aka fara ganin dogayen layukan mai a birnin tarayya Abuja da wasu sassan kasar na duk da cewa ‘yan kasar nan sun yi marhaban da matakin da Tinubun ya sanar a ranar Litinin din.

Tuni dai wasu ‘yan Nijeriya ma suka fara tofa albarkacin bakinsu a game da lamarin inda wasu ke ganin cewa bai kamata a dora laifin dogayen layuka da aka fara gani a kan gwamnati ba illa ‘yan kasuwa ne suka fara boye man don cin kazamar riba wasu kuma ke cewa ‘yan kasa ne suke nuna fargabar sayen mai suna karfafa wa ‘yan kasuwa wajen boyewa.

A wani bangare kuwa, a cikin wata sanarwa da shugabanta Festus Osifo da babban sakatare, Nuhu Toro suka sanya wa hannu, kungiyar ma’aikatan kamfanoni ta Nijeriya (TUC) ta bayyana cewa sabon shugaban kasa Bola Tinubu ba zai iya daukar matakin cire tallafin man fetur shi kadai ba kuma kamata ya yi ya dakata na dan lokaci don ba da damar tattaunawa mai karfi da tuntubar dukkan masu ruwa da tsaki, kafin yanke shawara kan batun janye tallafin man fetur.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

TUC ta kara da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su cikin ruwan sanyi da kuma warware su kafin shugaban ya yanke irin wannan shawara.

Idan ana iya tunawa dai tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya sha jaddada cewa za a janye tallafin man fetur a watan Yunin da za a shiga kuma ya kara karfafa batun a watan Afrilun da ya gabata, kuma masana sun ce bai kamata batun cire tallafin da sabon shugaba Tinubu ya yi a jawabinsa na ranar 29 ga watan Mayun ya shammaci ‘yan kasar nan ba sai dai kamata ya yi gwamnatin ta dauki dukkan matakan da suka dace don kawo sauki ga talaka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bola TinubuMan feturNNPCLTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Gana Da Shugaban EFCC A Fadar Shugaban Kasa

Next Post

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

2 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

10 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

11 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

12 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

15 hours ago
Next Post
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.