ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

by Sadiq
3 years ago
Mai

Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ya tabbatar da cewa akwai wadataccen mai da zai ishi ‘yan kasa na kimanin kwanaki 30 duk da cewa an fara ganin dogayen layukan mai tun da maraicen ranar Litinin.

Kungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (IPMAN), ta ce tabbas an fara ganin dogayen layukan mai kuma hakan baya rasa nasaba da furucin shugaba Tinubu amma sai mambobinta sun sayo mai daga NNPCL din a yau kafin ta iya magana a kan batun karin farashin da za a iya gani, lamarin da ya fara sanya fargaba a zukatan ‘yan Nijeriya.

  • Daga Karshe Dai, Cire Tallafin Mai Ya Tabbata, NNPC Na Sayar Da Lita N537 A Abuja
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

Jim kadan bayan ayyana janye tallafin man fetur da sabon shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi a jawabinsa bayan rantsar da shi ne, aka fara ganin dogayen layukan mai a birnin tarayya Abuja da wasu sassan kasar na duk da cewa ‘yan kasar nan sun yi marhaban da matakin da Tinubun ya sanar a ranar Litinin din.

ADVERTISEMENT

Tuni dai wasu ‘yan Nijeriya ma suka fara tofa albarkacin bakinsu a game da lamarin inda wasu ke ganin cewa bai kamata a dora laifin dogayen layuka da aka fara gani a kan gwamnati ba illa ‘yan kasuwa ne suka fara boye man don cin kazamar riba wasu kuma ke cewa ‘yan kasa ne suke nuna fargabar sayen mai suna karfafa wa ‘yan kasuwa wajen boyewa.

A wani bangare kuwa, a cikin wata sanarwa da shugabanta Festus Osifo da babban sakatare, Nuhu Toro suka sanya wa hannu, kungiyar ma’aikatan kamfanoni ta Nijeriya (TUC) ta bayyana cewa sabon shugaban kasa Bola Tinubu ba zai iya daukar matakin cire tallafin man fetur shi kadai ba kuma kamata ya yi ya dakata na dan lokaci don ba da damar tattaunawa mai karfi da tuntubar dukkan masu ruwa da tsaki, kafin yanke shawara kan batun janye tallafin man fetur.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

TUC ta kara da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su cikin ruwan sanyi da kuma warware su kafin shugaban ya yanke irin wannan shawara.

Idan ana iya tunawa dai tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya sha jaddada cewa za a janye tallafin man fetur a watan Yunin da za a shiga kuma ya kara karfafa batun a watan Afrilun da ya gabata, kuma masana sun ce bai kamata batun cire tallafin da sabon shugaba Tinubu ya yi a jawabinsa na ranar 29 ga watan Mayun ya shammaci ‘yan kasar nan ba sai dai kamata ya yi gwamnatin ta dauki dukkan matakan da suka dace don kawo sauki ga talaka.

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.