ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Wadataccen Mai Da Zai Ishi ‘Yan Kasa Nan Da Kwanaki 30 —NNPCL

by Sadiq
3 years ago
Mai

Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) ya tabbatar da cewa akwai wadataccen mai da zai ishi ‘yan kasa na kimanin kwanaki 30 duk da cewa an fara ganin dogayen layukan mai tun da maraicen ranar Litinin.

Kungiyar dillalan man fetur ta Nijeriya (IPMAN), ta ce tabbas an fara ganin dogayen layukan mai kuma hakan baya rasa nasaba da furucin shugaba Tinubu amma sai mambobinta sun sayo mai daga NNPCL din a yau kafin ta iya magana a kan batun karin farashin da za a iya gani, lamarin da ya fara sanya fargaba a zukatan ‘yan Nijeriya.

  • Daga Karshe Dai, Cire Tallafin Mai Ya Tabbata, NNPC Na Sayar Da Lita N537 A Abuja
  • Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

Jim kadan bayan ayyana janye tallafin man fetur da sabon shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi a jawabinsa bayan rantsar da shi ne, aka fara ganin dogayen layukan mai a birnin tarayya Abuja da wasu sassan kasar na duk da cewa ‘yan kasar nan sun yi marhaban da matakin da Tinubun ya sanar a ranar Litinin din.

ADVERTISEMENT

Tuni dai wasu ‘yan Nijeriya ma suka fara tofa albarkacin bakinsu a game da lamarin inda wasu ke ganin cewa bai kamata a dora laifin dogayen layuka da aka fara gani a kan gwamnati ba illa ‘yan kasuwa ne suka fara boye man don cin kazamar riba wasu kuma ke cewa ‘yan kasa ne suke nuna fargabar sayen mai suna karfafa wa ‘yan kasuwa wajen boyewa.

A wani bangare kuwa, a cikin wata sanarwa da shugabanta Festus Osifo da babban sakatare, Nuhu Toro suka sanya wa hannu, kungiyar ma’aikatan kamfanoni ta Nijeriya (TUC) ta bayyana cewa sabon shugaban kasa Bola Tinubu ba zai iya daukar matakin cire tallafin man fetur shi kadai ba kuma kamata ya yi ya dakata na dan lokaci don ba da damar tattaunawa mai karfi da tuntubar dukkan masu ruwa da tsaki, kafin yanke shawara kan batun janye tallafin man fetur.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

TUC ta kara da cewa akwai batutuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su cikin ruwan sanyi da kuma warware su kafin shugaban ya yanke irin wannan shawara.

Idan ana iya tunawa dai tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya sha jaddada cewa za a janye tallafin man fetur a watan Yunin da za a shiga kuma ya kara karfafa batun a watan Afrilun da ya gabata, kuma masana sun ce bai kamata batun cire tallafin da sabon shugaba Tinubu ya yi a jawabinsa na ranar 29 ga watan Mayun ya shammaci ‘yan kasar nan ba sai dai kamata ya yi gwamnatin ta dauki dukkan matakan da suka dace don kawo sauki ga talaka.

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

Za Mu Dauki Kwakkwaran Mataki Idan Gwamnati Ta Janye Tallafin Man Fetur —NLC

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.