• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Katafariyar Matatar Man Dangote Ga Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Rahotonni
0
Alfanun Katafariyar Matatar Man Dangote Ga Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabuwar matatar man dangote da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a farkon makon nan za ta kasance mai matukar alfanu ba ma kawai ga Nijeriya ba har da yankin Afirka baki daya. Kadan daga ciki shi ne yadda matatar za ta taimaka wa Nijeriya ceto dalar Amurka biliyan 30 da take kashewa wajen tace mai daga kasashen waje, tare da habaka shigo da kudaden kasashen waje akalla Dala biliyan 10.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da sauran shugabannin Afirka biyar suka ba da tabbacin Afirka za ta samu sa’ida wajen zuwa kasashen turawa sayo tataccen mai da kuma bunkasa hada-hadar kasuwanci. Shi kansa Shugaba Muhammadu Buhari ya ce matatar za ta taimaka wajen ciyar da Nijeriya gaba ta fuskar dogaro da kai da samar da abinci, da dai sauran muradun kasa.

  • Sin Ta Bukaci A Tallafawa AU Kan Aikin Wanzar Da Zaman Lafiya

Da yake jawabi a wurin kaddamar da rukunin matatar man ta Dangote da ke Legas a ranar Litinin, 22 ga watan Mayu, 2023, gwamnan babban bankin CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana cewa matatar Dangote da ke da karfin sarrafa gangar danyen mai 650,000 a kowace rana ita ce matatar mai mafi girma a duniya kuma za ta kara habaka samun kudaden waje wanda zai kara karfafa asusun ajiyar gwamnati da kuma daidaita farashin kudaden musaya.

Ya lura cewa, ana sa ran tasirin ajiyar zai fito fili baro-baro a cikin asusun ajiyar Nijeriya na waje ta hanyar rage matsin lamba kan ma’aunin biyan kudi, yana mai cewa “har ila yau akwai fa’idodi masu yawa da za mu samu daga fitar da kayan da matatar za ta rika sarrafawa tana fitawar zuwa sauran duniya.

“Bugu da kari matatar man za ta taimaka wa Nijeriya wajen tsumin dalar Amurka biliyan 30 da ake kashewa wajen shigo da man fetur, sannan ana hasashen tattalin arzikin kasar zai amfana da karin dalar Amurka biliyan 10 na kudaden musaya a duk shekara ta hanyar fitar da tataccen man fetur zuwa kasashen waje, wanda hakan zai kara habaka asusun ajiyarmu a hukumance da saukaka wahlhalun da ake sha na musayar musayar kudi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

“Wannan aikin zai kuma ba da tallafi ga ayyukan kasafin kudi na gwamnati kamar yadda zai taimaka wajen saukaka matsalolin makudan kudin da ake warewa a kan tallafin man fetur da kuma samar da tanadin kasafin kudi mai inganci. Bayanai da ake samu sun nuna cewa, a cikin shekaru biyar, tallafin man fetur a Nijeriya ya haura sama da ninki tara daga kimanin Naira biliyan 154 a shekarar 2017 zuwa sama da Naira Tiriliyan 1.43, kafin ya kuma tashi zuwa Naira Tiriliyan 4.4 a karshen shekarar 2022.

“Hasashen na nuna cewa wannan adadi zai iya zarce Naira tiriliyan 7 a cikin shekaru uku masu zuwa idan ba mu magance shi yadda ya kamata ba. Alhamdu lillahi, matatar mai ta Dangote za ta iya ceto wa Nijeriya kimanin Naira Tiriliyan 5 zuwa Naira Tiriliyan 7 a duk shekara a cikin kasafin kudin Gwamnatin Tarayya nan da shekaru biyar masu zuwa,” in ji shi.

A halin da ake ciki, Emefiele ya bayyana cewa, rukunin Dangote ya fara biyan wasu lamunin kasuwanci tun kafin kaddamar da wannan cibiyar wanda ya ce yana nuna iya kasuwancin kamfanin da shugabansa. Bayan biyan wani kaso mai yawa, basusuka sun ragu sosai daga sama da dala biliyan 9 zuwa dala biliyan 3.

“A daidai wannan lokaci dole ne in yaba wa dukkan bankunan Nijeriya da ke cikin gida, wadanda ba wai kawai sun hada hannu da aikin ta hanyar samar da kudade masu inganci ba, amma suna da masaniya kan muhimmancin aikin ga al’ummarmu. Sun ba da tallafi mai yawa da fahimta ta musamman, hatta lokacin biyan kudin ruwa da adadin abin da za a rika biya sun ragu sosai,” in ji shi.

A nasa jawabin, shugaba Buhari, ya ce matatar man Dangote ta kara nuna jajircewar Alhaji Aliko Dangote, inda ya kara da cewa kamfanin zai ciyar da Nijeriya gaba wajen dogaro da kai wajen samar da abinci, da dai sauran muradun kasa.

A cewarsa, matatar mai ta Dangote da ke zama matatar mai mafi girma a Nahiyar Afirka, tare da masana’antar takin zamani, za ta taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen aikin noma a matsayin sana’a ta ainihi da ake cin gajiyarta koyaushe da kuma bayar da gudunmawa wajen daidaita harkar man fetur a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci A Tallafawa AU Kan Aikin Wanzar Da Zaman Lafiya

Next Post

Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

4 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 week ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.