• Leadership Hausa
Saturday, June 3, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alfanun Katafariyar Matatar Man Dangote Ga Nijeriya

by Abubakar Abba
1 week ago
in Rahotonni
0
Alfanun Katafariyar Matatar Man Dangote Ga Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sabuwar matatar man dangote da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a farkon makon nan za ta kasance mai matukar alfanu ba ma kawai ga Nijeriya ba har da yankin Afirka baki daya. Kadan daga ciki shi ne yadda matatar za ta taimaka wa Nijeriya ceto dalar Amurka biliyan 30 da take kashewa wajen tace mai daga kasashen waje, tare da habaka shigo da kudaden kasashen waje akalla Dala biliyan 10.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da sauran shugabannin Afirka biyar suka ba da tabbacin Afirka za ta samu sa’ida wajen zuwa kasashen turawa sayo tataccen mai da kuma bunkasa hada-hadar kasuwanci. Shi kansa Shugaba Muhammadu Buhari ya ce matatar za ta taimaka wajen ciyar da Nijeriya gaba ta fuskar dogaro da kai da samar da abinci, da dai sauran muradun kasa.

  • Sin Ta Bukaci A Tallafawa AU Kan Aikin Wanzar Da Zaman Lafiya

Da yake jawabi a wurin kaddamar da rukunin matatar man ta Dangote da ke Legas a ranar Litinin, 22 ga watan Mayu, 2023, gwamnan babban bankin CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana cewa matatar Dangote da ke da karfin sarrafa gangar danyen mai 650,000 a kowace rana ita ce matatar mai mafi girma a duniya kuma za ta kara habaka samun kudaden waje wanda zai kara karfafa asusun ajiyar gwamnati da kuma daidaita farashin kudaden musaya.

Ya lura cewa, ana sa ran tasirin ajiyar zai fito fili baro-baro a cikin asusun ajiyar Nijeriya na waje ta hanyar rage matsin lamba kan ma’aunin biyan kudi, yana mai cewa “har ila yau akwai fa’idodi masu yawa da za mu samu daga fitar da kayan da matatar za ta rika sarrafawa tana fitawar zuwa sauran duniya.

“Bugu da kari matatar man za ta taimaka wa Nijeriya wajen tsumin dalar Amurka biliyan 30 da ake kashewa wajen shigo da man fetur, sannan ana hasashen tattalin arzikin kasar zai amfana da karin dalar Amurka biliyan 10 na kudaden musaya a duk shekara ta hanyar fitar da tataccen man fetur zuwa kasashen waje, wanda hakan zai kara habaka asusun ajiyarmu a hukumance da saukaka wahlhalun da ake sha na musayar musayar kudi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

“Wannan aikin zai kuma ba da tallafi ga ayyukan kasafin kudi na gwamnati kamar yadda zai taimaka wajen saukaka matsalolin makudan kudin da ake warewa a kan tallafin man fetur da kuma samar da tanadin kasafin kudi mai inganci. Bayanai da ake samu sun nuna cewa, a cikin shekaru biyar, tallafin man fetur a Nijeriya ya haura sama da ninki tara daga kimanin Naira biliyan 154 a shekarar 2017 zuwa sama da Naira Tiriliyan 1.43, kafin ya kuma tashi zuwa Naira Tiriliyan 4.4 a karshen shekarar 2022.

“Hasashen na nuna cewa wannan adadi zai iya zarce Naira tiriliyan 7 a cikin shekaru uku masu zuwa idan ba mu magance shi yadda ya kamata ba. Alhamdu lillahi, matatar mai ta Dangote za ta iya ceto wa Nijeriya kimanin Naira Tiriliyan 5 zuwa Naira Tiriliyan 7 a duk shekara a cikin kasafin kudin Gwamnatin Tarayya nan da shekaru biyar masu zuwa,” in ji shi.

A halin da ake ciki, Emefiele ya bayyana cewa, rukunin Dangote ya fara biyan wasu lamunin kasuwanci tun kafin kaddamar da wannan cibiyar wanda ya ce yana nuna iya kasuwancin kamfanin da shugabansa. Bayan biyan wani kaso mai yawa, basusuka sun ragu sosai daga sama da dala biliyan 9 zuwa dala biliyan 3.

“A daidai wannan lokaci dole ne in yaba wa dukkan bankunan Nijeriya da ke cikin gida, wadanda ba wai kawai sun hada hannu da aikin ta hanyar samar da kudade masu inganci ba, amma suna da masaniya kan muhimmancin aikin ga al’ummarmu. Sun ba da tallafi mai yawa da fahimta ta musamman, hatta lokacin biyan kudin ruwa da adadin abin da za a rika biya sun ragu sosai,” in ji shi.

A nasa jawabin, shugaba Buhari, ya ce matatar man Dangote ta kara nuna jajircewar Alhaji Aliko Dangote, inda ya kara da cewa kamfanin zai ciyar da Nijeriya gaba wajen dogaro da kai wajen samar da abinci, da dai sauran muradun kasa.

A cewarsa, matatar mai ta Dangote da ke zama matatar mai mafi girma a Nahiyar Afirka, tare da masana’antar takin zamani, za ta taimaka wa ‘yan Nijeriya wajen aikin noma a matsayin sana’a ta ainihi da ake cin gajiyarta koyaushe da kuma bayar da gudunmawa wajen daidaita harkar man fetur a kasar.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bukaci A Tallafawa AU Kan Aikin Wanzar Da Zaman Lafiya

Next Post

Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

Related

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya
Rahotonni

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

19 hours ago
Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata
Rahotonni

Yadda Amurka Ta Yi Kokarin Amfani Da Nukiliya Wajen Tarwatsa Wata

4 days ago
Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya
Rahotonni

Yadda Cutar Hawan Jini Ke Kisan Mummuke A Nijreriya

6 days ago
Wata Kungiyar Siyasa Ta Yi Allah Wadai Da Rusau A Jihar Kaduna
Rahotonni

Ragargazar Sallama Da El-Rufa’i Ke Yi A Kaduna

6 days ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan
Rahotonni

Zaki Da Dacin Mulkin Shugaba Buhari

7 days ago
Hukumar Aikin Hajji Ta Warware Sarkakiyar Karin Kudi Ga Maniyyata
Rahotonni

Hukumar Aikin Hajji Ta Warware Sarkakiyar Karin Kudi Ga Maniyyata

1 week ago
Next Post
Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

Xi Jinping Na Fatan Sin Da Janhuriyar Dimokuradiyyar Congo Za Su Yi Aiki Tare Wajen Bunkasa Ci Gaba Da Samar Da Makoma Ta Gari

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Tinubu Na Ganawa Ta Farko Da Shugabannin Tsaro

An Fara Kunfar Baki Yayin Da Tinubu Ya Fara Nada Mukamai

June 3, 2023
Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

Xi Jinping Ya Jaddada Bukatar Gina Kasar Sin Mai Wayewar Kai Ta Zamani

June 2, 2023
Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Korafinta Dangane Da Yarjejeniyar Cinikayya Da Aka Kulla Tsakanin Amurka Da Taiwan

June 2, 2023
Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

Taron Tattaunawar Shangri-La Ya Nuna Ra’ayin Tabbatar Da Zaman Lafiya Na Sin

June 2, 2023
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

June 2, 2023
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

June 2, 2023
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

June 2, 2023
An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

June 2, 2023
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

June 2, 2023
RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

RCEP Ta Fara Aiki A Kasashe 15 Da Suka Sa Hannu Kan Yarjejeniyar

June 2, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.