• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Amurka Ba Ta Sauya Ba Ko Kadan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa kan ce “duniya juyi-juyi ne “. To, yau za mu tattauna batun da ya shafi juyi-juyi, ko kuma sauyin, da ke faruwa a duniya.

Yanzu haka ana iya ganin sauyawar yanayi dangane da kasar Amurka: Bayan da shugaba Donald Trump ya koma fadar shugabancin kasar Amurka ta White House, kasar ta riga ta janye jiki daga hukumomin kasa da kasa da suka hada da majalisar kare hakkin dan Adam dake karkashin Majalisar Dinkin Duniya, da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da yarjeniyoyin da suka hada da yarjejeniyar tinkarar sauyin yanayi ta Paris, da ta tsara ayyukan tinkarar sauyin yanayi ta Majalisar Dinkin Duniya, ta yadda kasar ta yi watsi da nauyin dake wuyanta a cikin wadannan hukumomi da yarjeniyoyin kasa da kasa. Ban da haka, matakan da Amurka din ta dauka a cikin gida na korar da ‘yan kasashen waje, da rufe hukumar raya kasa da kasa ta Amurka ta USAID suna mummunan tasiri kan kasashen Afirka. Idan mun dauki kasar Najeriya a matsayin misali, za mu ga yadda aka tsare ‘yan Najeriya fiye da dubu 200 a kasar Amurka, wadanda za a iya maida su gida. Kana dakatar da aikin USAID ita ma ta haddasa gibin kudin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan tinkarar cutar kanjamau, da ta tibi, da ta zazzabin cizon sauro, a kasar ta Najeriya.

  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samar Da Tirela 300 Na Abinci Don Rabo Da Azumi

Sai dai sauyawar manufofi ba ta nufin canzawar halayyar kasar Amurka. Hakika yadda Amurka din ta yi fatali da nauyinta a cikin hukumomin kasa da kasa, da aikin kulawa da ‘yan kasashen waje, da tallafin da take samar wa sauran kasashe, ya nuna cewa, kasar sam ba ta canza manufarta ta daukar matakan kashin kai ba. Dangane da batun, jaridar Daily Trust ta kasar Najeriya ta ce abun da kasar Amurka ta yi, shi ne cire “rigarta” ta karamci. Yayin da a nata bangare, jaridar The Independent ta kasar Uganda ta ce yadda aka rufe hukumar USAID yana da kyau, saboda kasar Amurka ta dade tana amfani da hukumar wajen bayyana kanta a matsayin wata kasa “mai tausayi”, inda aka rubuta cewa, “Kasar Amurka ta ware dala kusan biliyan 900 duk shekara ga bangaren aikin soja, don jefa boma-bomai da kashe fararen hula a wurare daban daban, yayin da a nata bangaren hukumar USAID ta kashe dala biliyan 40 a kowace shekara, sa’an nan ta sanya mutane da yawa amincewa da matsayin kasar Amurka na ‘mai tausayi’.” To, daga yin kisa yadda ta ga dama, da neman samun fin karfi da yin babakere, zuwa yin fatali da nauyin dake wuyanta, da mai da moriyar kasar Amurka gaban ta sauran kasashe, anya ana iya ganin sauyawar halayyar kasar Amurka a ciki? A ‘a, sam ba za a gani ba.

Saboda haka, ya kamata kasashe masu tasowa su dauki matakai don tinkarar manufofin kasar Amurka na kashin kai, wadanda ba za ta taba canzawa ba, maimakon mai da hankali kan wasu manufofin kasar na gajeren lokaci, wadanda ke sauyawa har kullum. Amma ta yaya za a iya tinkarar manufar kasar ta kashin kai? Shawara daga kasar Sin ita ce, a dauki manufar cudanyar sassa daban daban.

Ma’anar manufar ita ce, a yi kokarin samar da dabarar daidaita al’amura ta hanyar tattaunawa. Kana bangarori daban daban su samu damar tsara ka’idoji, wadanda za a bi su tare. Ban da haka, bai kamata a ba kasashe kalilan ikon tillastawa sauran kasashe wasu ka’idoji, ko kuma ba wasu kasashe masu karfi ikon ba da umarni ba. Tsakanin manufar nan da ta kashin kai, za a ga wata na dora muhimmanci kan hadin kai, yayin da wata ke daukaka fin karfi da ja-in-ja. Saboda haka cikin sauki za a iya bambance su, da ganin wanne ne daga cikinsu ya fi nuna yanayi na adalci.

Labarai Masu Nasaba

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

Ban da haka, idan mun mai da hankali kan cudanyar kasashe daban daban, da zamansu tare a cikin duniya, za mu san huldar da ake da ita tare da Amurka, wani bangare ne kawai na huldar kasa da kasa. Saboda haka, yayin da wata kasa ta gamu da matsala, idan wata kasa ta nade hannu, ba ta son ba da taimako, tabbas ba za a rasa bangarorin da ke son samar da taimakon ba. Matukar an yi kokarin kulla abokantaka bisa ra’ayi na daidaiwa daida, da amfanawa kowa, to, tabbas ba za a rasa abokin hulda ba.

Sai dai idan mun nazarci sabbin matakan gwamnatin kasar Amurka, za mu ga kusan dukkansu na da nufin tsimin kudi da tabbatar da karin kudin shiga, inda ake iya ganin alamar sauyawar matsayin kasar daga mai cikakken yakini zuwa mai ra’ayin rikau, har ma ta yi watsi da kimarta da kwarjininta. Dalilin da ya sa Amurka yin haka, shi ne, ci gaban kasashe masu tasowa bisa hadin gwiwarsu na haifar da ainihin sauyawar yanayi ga tsare-tsaren kasa da kasa. (Bello Wang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Taya Babban Editan LEADERSHIP, Ishiekwene Murnar Cika Shekaru 60

Next Post

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Related

Daurarru
Ra'ayinmu

Bukatar Inganta Rayuwar Daurarru A Gidajen Yarin Kasar Nan

3 weeks ago
NCC
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Karin Kudin Kiran Waya Da Na Data

2 months ago
Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
Ra'ayi Riga

Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi

3 months ago
Ra'ayinmu

Gangamin Yaki Da Cutar Kuturta A Nijeriya

3 months ago
Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya
Ra'ayinmu

Karuwar Cin Zarafi Da Makomar Yara A Nijeriya

5 months ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Ra'ayinmu

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

5 months ago
Next Post
Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

Juyin-juya-halin Kyautata Muhalli: Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Samar Da Makoma Mai Kyau

LABARAI MASU NASABA

Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

Warware Basussuka: WAEC DA NECO Sun Saki Sakamakon Ɗaliban Zamfara Na Shekara Biyar

May 25, 2025
Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

Shekaru 10, Kofuna 16 Kevin De Bruyne Ya Yi Bankwana Da Manchester City

May 25, 2025
An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.