• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnain Tarayya Ta Sake Inganta Harkokin Amfanin Gona

by Abubakar Abba
1 year ago
Tarayya

An bukaci gwamnatin tarayya ta inganta sake habaka harkokin amfanin gona, domin samun damar fitar da shi zuwa kasashen waje, kana gwamnatin ta fi mayar da hankali kan gudanar da ayyukan da za su kara habaka fannin; baya ga man fetir da kusan shi kadai ake iya fitar da shi zuwa kasashen na ketare.

Wasu kwararru ne suka bayar da wannan shawara, a taron shekara karo na tara; a wajen baje kolin da bankin Zenith ya shirya.

  • Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
  • Zaben Kananan Hukumomi: Gwamnoni Na Tozarta Dimokuradiyya – Jam’iyyun Adawa

Taken taron shi ne, ‘Fitar da kayan amfanin gona zuwa kasashen, baya ga man fetir; domin kara farfado da fannin’.

Sun sanar da cewa, Nijeriya za ta iya amfana da kashi 70 na yawan matasan da ke kasar ta hanyar hada-hadar musaya.

Daya daga cikin kwararrun, Obiora Madu ya ce, “Kashi 70 na yawan al’ummar Nijeriya, matasa ne; wanda hakan ya sanya muke da karfin da za mu iya gudanar da ayyuka masu yawan gaske a kasuwar duniya”.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Madu ya kara da cewa, akwai bukatar kara wayar da kai; domin fadakarwa a kan ayyukan fitar da kaya zuwa kasashen ketare, musamman a kan amfanin gona.

Wata kididdigar tattalin arzikin kasar a zango na biyu ta yi nuni da cewa, jimillar kayan da ba su shafi fannin mai fetir a Nijeriya ba a 2024, ta kai dala 1.2, daidai da Naira biliyan 1.8, wanda hakan ya nuna cewa, ta kai yawan kashi 9.28 na jimillar kayan da aka fitar a cikin wannann shekara.

Haka zalika, bisa fashin bakin da aka yi na wannan kididdiga ta nuna cewa, fannin da bai shafi man fetir ba; shi ne kan gaba wajen ciyar da cibiyoyin hada-hadar kudi na kasar gaba tare da samar da bayanai kan amfanin gona, kasuwanci da kuma kayan da ake sarrafawa.

Fannin da bai shafi man fetir din kuma ba, ya samar da kashi 94.30 ga tattalin arzikin Nijeriya a zango na biyun 2024, wanda ya yi kasa da kashi 93.62 a 2023, hakan ya nuna cewa; ya kai kashi 94.66 sama da wanda aka samu a zango na farko a 2024, da ya kai kashi 93.62.

Shi ma a nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar noma da samar da wadacaccen abinci, Otunba Faseru na Jihar Osun ya sanar da cewa, dole ne Nijeriya ta karfafa mayar da hankali kan noma, domin samun riba.

“Muna da komai da za mu iya habaka fannin aikin noma a wannan kasa, domin kuwa Allah ya albarkace mu da wadatacciyar kasar noma mai kyau, ga shi kuma muna da ruwan da za mu iya yin noma da shi har sau biyu a shekara”.

A jawabinta na maraba, Manajan Darakta kuma babbar jami’a a bankin Zenith, Adaora Umeoji; ta sanar da muhimmancin da ke tattare da fannin da bai shafi harkokin man fetir ba, musamman wajen kara samar da ayyukan yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

An Samu Karin Yawan Hannun Jari A Aikin Noma Da Kashi 226 Cikin Wata Uku

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.