• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai

by Umar Faruk
3 years ago
in Labarai
0
An Dakatar Da Mu Don Mun Nemi Mukamin Alkalin Babbar Kotun Kebbi – Wasu Alkalai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alkalan Kotun Majistare uku da aka dakatar kuma aka maida su shelkwatar gidan shari’a a Jihar Kebbi, sun roki hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) da ta shiga tsakani kan lamarin da ya kai ga dakatar da su saboda nuna sha’awarsu na neman mukamin Alkalin Babbar kotun jihar.

Alkalan da abin ya shafa, wadanda suka bayyana dakatarwar tana a matsayar cin zarafi kuma da bata masu tahirin aiki a gidan shari’a, sun roki NJC da ta taimaka wani bincike da tantance tare da bayyana gaskiyar lamarin kan neman mukamin Alkalin Babbar kotun Jihar da suka yi wanda ya sanya ana yi musu bita da kulli.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Jam’iyyar PDP A Kebbi Ta Shirya Tarbar Dan Takarar Shugaban Kasa, Atiku Abubakar

Wakilinmu ya ce wadanda abin ya shafa sun hada da: Babban Majistare Mustapha Umar-Maccido, Babban Kotun Majistare da ke Kalgo, Majistare Umar Salihu-Kokani, Babban Kotun Majistare ta uku da ke Birnin Kebbi da Majistare Halima Umar, Babban Kotun Majistare ta biyu da ke Birnin Kebbi.

Har ila yau, bisa ga rahotanni sun ce an dakatar da Majistare Umar-Maccido ne bisa zarginsa da laifin gujewa daga aiki da gudanar da ayyukan lauyanci a wasu kotutun a wasu jihohin kasar cikin a sirri, an kuma kiran Majistare Salihu-Kokani zuwa hedikwatar gidan Shari’a ta jihar ​​bisa zarginsa da mari wani lauyan gwamnati, Abdullahi Bawa-Dan-Bauchi, wanda solisita janaral ya rubuta korafi akansa.

Haka kuma Majistare Halima Umar itama an yi mata kiraye zuwa hedikwata ​​bisa zarginsa da aikata laifin sakin barayin shanu akan beli.

Labarai Masu Nasaba

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Idan za a iya tunawa, a ranar 14 ga Oktoba, 2022, babban magatakardar babbar kotun jihar Kebbi, Hussain Abdullahi-Zuru ya sanar da dakatar da Alkalin Mustapha Umar-Maccido da Alkalai Umar-Salihu Kokani ta wata sanarwa da ya sanya wa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi.

Da ya ke zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi a madadin Alkalan ukun da lamarin ya shafa Majistare Umar-Maccido ya danganta abin da ya faru da su da irin sha’awar da suka nuna a kan mukaman manyan alkalan kotunan shari’a na jihar ta hanyar shigar da takardun su na nuna suna neman zama Babban Alkalan Babbar kotun Jihar watau (High court judges).

Ya ce, an tilasta musu yin magana da ‘yan jarida ne saboda hukumar da abin ya shafa ta yi gaggawar garzayawa kafafen yada labarai don bata musu suna, maimakon a sasanta lamarin cikin ruwan sanyi ta hanyar amfani da hanyoyin da suka dace da doka ta gidan Shari’a idan har neman mukamin Alkalin Babbar kotun Jihar laifi ne, inji shi.

Kazalika ya kara da cewa, “Duk wadannan matsalolin sun samo asali ne sakamakon sha’awar da muka nuna na daukaka matsayin alkalan babbar kotuna jihar. Duk zargin da ake mana ba gaskiya ba ne, inji Majistare Mustapha Umar Maccido”.

“A makon da ya gabata ne aka dakatar da Majistare Halima Umar ta Kotun Majistare ta Biyu da ke Birnin Kebbi, bisa wani batu da ake zargin ta bayar da belin barayin shanu.

“Wannan laifin babban laifi ne wanda ya kai shekaru 14 a gidan yari ba tare da belin ba, wanda ba ta da huruminsa. Wannan shine bayanin da muka samu daga Cif Registara da kansa a wata tattaunawa ta gidan radiyo na tsawon awa daya.

“Amma duk waɗannan kame-kame ne, ba gaskiya ba ne. Akwai batutuwa da yawa masu alaƙa da waɗannan duka. Wani muhimmin al’amari shi ne, ni da Majistare Umar Salihu Kokani da Majistare Halima Umar, duk mun nuna sha’awar a daukaka matsayinmu zuwa alkalan Kotuna Jihar, wanda hakkinmu ne, a duk lokacin da aka fitar da sanarwar gurabun mukamin Alkalin Babbar kotun mu nema saboda matsayinmu ya kai na mu nema,” inji Majistare Mustapha Umar Maccido.

“Kuma ka’idojin NJC a fili take, a cikin ka’idar NJC ta shekarar 2014 na nadin mukamai na ma’aikatan shari’a wanda ya bukaci a rika tallata guraben da ake da su a babban kotun Jihar.

“Haka kuma, wannan ka’ida ta bukaci a aika da tallar zuwa jihohi 36 na tarayya da kuma babban birnin tarayya Abuja domin sanar da duk ‘yan asalin jihar Kebbi da ke kowace jiha masu sha’awar neman mukaman.”

A cewarsa, ta wannan kafar ne hukumar shari’a ta jihar za ta iya fitar da ‘yan takarar da ba su cancanta ba. Ya ci gaba da bayyana cewa akasin haka, ba su bi ka’idojin hukumar NJC da ta ce dole ne su tallata guraben ba.

“Sai dai sun buga wata ‘yar karamar takarda a kusurwa daya a hedikwatar babbar kotun jihar Kebbi, Birnin Kebbi, suka manna wata a kotun daukaka kara ta Shari’a inda babu Lauya.

“Ba su yi wa shugaban kungiyar lauyoyin Nijeriya (NBA) reshin Jihar kwafi ba, ba su mika wa shugaban kungiyar majistare ta kasa (MAN) reshin jihar Kebbi kwafin ba. Don haka, ba su tallata shi ba kamar yadda shawarar NJC ta bayar.

“Don haka da wannan muka yi imanin cewa Babbar jojin Jihar Kebbi ya saba ka’idar NJC wadda ba bisa tsarin ba ne. Ba wai kawai tsarin tallan ya kamata ya kasance na kwanaki 21 ko makonni biyu ba, amma sun lika tallar su a ranar 5 ga Oktoba, kuma sun cire shi a ranar 6 ga Oktoba, kuma wa’adin da aka bayar a cikin tallan ya kasance 7 ga Oktoba, ga masu sha’awar.

“Wato ma’ana, sun ba da kuraren lokaci kwana ne domin su maye gurbin da ke akwai na batare da wasu sun nema. Saboda haka muna ganin cewa tsarin na yaudara kawai, inji Majistare Mustapha Umar Maccido”.

“Duk dakatarwar aka yi muna saboda mun nemi mukaman Babbar Alkalin Babbar kotun Jihar ne. Wannan shi ne kawai dalili. Domin daidaituwa, wannan ba zai iya faruwa kawai ba. Na nema, ya nema kuma ta nema kuma mu kadai ne ke fuskantar wannan dakatarwar da cin zarafi a duk cikin Majistare na Jihar, in ji Mustapha Umar-Maccido”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlkalaiKebbiKokawaKotuNCJNeman Mukami
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Jadawalin Gasar Cin Kofin Duniya Na Mata

Next Post

Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

Related

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

18 minutes ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

5 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

6 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

7 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

8 hours ago
Next Post
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

Kungiyar 'Yan Jarida Ta Raba Gari Da Gwamnatin Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.