ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

by Sadiq
3 years ago
Matashi

Wata kotu a yankin Kado da ke Abuja, ta yanke wa wani matashi mai shekaru 24, mai suna Micheal Ayegh, mai shekaru 24 hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari, bisa samunsa da laifin hada baki da kuma satar injin janareta wanda kudinsa ya kai N550,000.

Matashin da ya fito daga jihar Nasarawa, ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, ya kuma roki kotun da ta yi masa sassauci.

  • Zaben Gwamnoni: Wasu Na Kitsa Makarkashiyar Bata Sunan Gwamnan Gombe —APC
  • Na Kalubalanci Tsarin Da Ya Ayyana Tinubu A Matsayin Shugaban Kasa -Peter Obi

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a Muhammed Wakili ya ce, ya yanke wa wanda ake kara hukunci ne bisa la’akari da laifin da ya yi.

ADVERTISEMENT

“Kotu ta samu wanda ake tuhuma da aikata laifin, bisa ga rokon da ya yi na a yi masa rangwame, wanda shi ne karon farko da ya yi laifin da bai bata lokacin kotu ba.

“An yanke wa Micheal Ayegh hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari tare da zabin biyan tarar N20,000, in ji alkalin.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Lauyan mai shigar da kara, Stanley Nwafoaku, ya roki kotun da ta biya diyya N550,000 kasancewar darajar janaretan da aka sace.

Sai dai alkalin kotun ya amince da bukatar sannan ya umarci wanda aka yanke wa hukuncin biyan diyya N550,000 ga wanda ya kai karar.

Ya ce hukuncin zai zama izina ga masu son aikata duk wani laifi.

Tun da farko dai lauyan mai shigar da kara ya shaida wa kotun cewa, an gurfanar da wanda ake tuhumar ne a kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi hada baki da kuma sata.

Nwafoaku ya ce a ranar 28 ga watan Fabrairu da misalin karfe 9:30 na dare, mai shigar da kara Mista Iheanacho Anayo na yankin Danziyal Plaza Central Abuja, ya kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sanda na Mabushi.

Ya yi zargin cewa a ranar 10 ga watan Fabrairu da misalin karfe 8:30 na dare, wanda ake tuhumar ya hada baki da wani tare da sace janareta mallakin wanda ya kai karar.

Nwafoaku ya ce yayin binciken ‘yan sanda wanda ake kara ya amince da aikata laifin.

Lauyan mai gabatar da kara ya bayyana cewa laifin ya ci karo da tanadin sashe na 97 da 288 na dokar laifuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Next Post
Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.