• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kotu a yankin Kado da ke Abuja, ta yanke wa wani matashi mai shekaru 24, mai suna Micheal Ayegh, mai shekaru 24 hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari, bisa samunsa da laifin hada baki da kuma satar injin janareta wanda kudinsa ya kai N550,000.

Matashin da ya fito daga jihar Nasarawa, ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, ya kuma roki kotun da ta yi masa sassauci.

  • Zaben Gwamnoni: Wasu Na Kitsa Makarkashiyar Bata Sunan Gwamnan Gombe —APC
  • Na Kalubalanci Tsarin Da Ya Ayyana Tinubu A Matsayin Shugaban Kasa -Peter Obi

Da yake yanke hukunci, Mai shari’a Muhammed Wakili ya ce, ya yanke wa wanda ake kara hukunci ne bisa la’akari da laifin da ya yi.

“Kotu ta samu wanda ake tuhuma da aikata laifin, bisa ga rokon da ya yi na a yi masa rangwame, wanda shi ne karon farko da ya yi laifin da bai bata lokacin kotu ba.

“An yanke wa Micheal Ayegh hukuncin daurin watanni 12 a gidan yari tare da zabin biyan tarar N20,000, in ji alkalin.

Labarai Masu Nasaba

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Lauyan mai shigar da kara, Stanley Nwafoaku, ya roki kotun da ta biya diyya N550,000 kasancewar darajar janaretan da aka sace.

Sai dai alkalin kotun ya amince da bukatar sannan ya umarci wanda aka yanke wa hukuncin biyan diyya N550,000 ga wanda ya kai karar.

Ya ce hukuncin zai zama izina ga masu son aikata duk wani laifi.

Tun da farko dai lauyan mai shigar da kara ya shaida wa kotun cewa, an gurfanar da wanda ake tuhumar ne a kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi hada baki da kuma sata.

Nwafoaku ya ce a ranar 28 ga watan Fabrairu da misalin karfe 9:30 na dare, mai shigar da kara Mista Iheanacho Anayo na yankin Danziyal Plaza Central Abuja, ya kai rahoton lamarin a ofishin ‘yan sanda na Mabushi.

Ya yi zargin cewa a ranar 10 ga watan Fabrairu da misalin karfe 8:30 na dare, wanda ake tuhumar ya hada baki da wani tare da sace janareta mallakin wanda ya kai karar.

Nwafoaku ya ce yayin binciken ‘yan sanda wanda ake kara ya amince da aikata laifin.

Lauyan mai gabatar da kara ya bayyana cewa laifin ya ci karo da tanadin sashe na 97 da 288 na dokar laifuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JanaretaKotuMatashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Gwamnoni: Wasu Na Kitsa Makarkashiyar Bata Sunan Gwamnan Gombe —APC

Next Post

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

Related

Matashi
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

2 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

2 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

3 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

3 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

4 hours ago
Matashi
Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

5 hours ago
Next Post
Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

Shugabanci Na Gari Shi Ne Sirrin Zaman Lafiya Da Ci Gaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Matashi

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Matashi

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.