• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi

by Sadiq
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An daure Ministar gwamnatin Uganda a kurkuku a lamarin da ba a saba gani na rashawa da ya shafi manyan jami’ai, inda ake zarginta da sama da fadi da kwanon rufi da aka tanada don gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja na Arewacin kasar.

An tuhumi Mary Goretti Kitutu, Ministar Kula da Harkokin Karamoja da dan uwanta Michael Naboya Kitutu bisa damfarar gwamnati.

  • Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON
  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda ta bayyana cewa ana tuhumar ‘yan uwan biyu da hada baki a damfarar gwamnati wajen sama da fadi da kayan da aka sayo don amfanin mutane marasa galihu a yankin Karamoja.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta kara da cewa an tsare ministar a kurkuku har nan da ranar 12 ga Afrilu.

A ranar Alhamis ne dai Minista Mary Goretti Kitutu da dan uwanta suka gurfana a gaban Kotun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

An sayo kwanukan rufin don amfani da su wajen gina gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja, yankin da ke fama da rashin ci gaba, kuma yake fama da matsaloli a Arewa Maso Yammacin Uganda kusa da iyakar kasashen Kenya da Sudan ta Kudu.

Wannan abun kunya ya janyo ce-ce-ku-ce da kokawar jama’a da dama a kasar da cin hanci da rashawa suka yi wa gwamnatinta katutu.

Abu ne da ba a saba gani ba na gurfanar da babban mai rike da mukamin siyasa saboda zargin cin hanci da rashawa, kuma Kitutu ce jami’a mafi girman mukami da aka gurfanar a gaban kotu a ‘yan shekarun nan.

Abu mai kama da wannan da ya faru shi ne na 2007, lokacin da aka tuhumi wasu jami’an gwamnati biyu; Jim Muhwezi da Mike Mukula da sama da fadin miliyoyin daloli na bayar da agaji.

Madugun ‘yan adawar Uganda Bobi Wine ya ce tuhumar Kitutu ‘Da walakin ne’, ya kuma zargi gwamnatin Yoweri Museveni da zama mafi muni wajen aikata cin hanci da rashawa.

Mawakin da ya zama dan takarar shugaban kasa ya ce “Kamata ya yi dukkan mambobin gwamnatin Museveni da shi kansa su kasance a cikin kurkuku saboda cin hanci da rashawa”.

Ya kara da cewa “ba za mu yi murnar tuhuma kan kwanon rufi ba a lokacin da ake almabazzaranci da biliyoyin daloli.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistaUgandaZargin Sata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tinubu Na Son Dawo Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN

Next Post

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

15 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

2 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

7 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.