• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi

by Sadiq
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An daure Ministar gwamnatin Uganda a kurkuku a lamarin da ba a saba gani na rashawa da ya shafi manyan jami’ai, inda ake zarginta da sama da fadi da kwanon rufi da aka tanada don gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja na Arewacin kasar.

An tuhumi Mary Goretti Kitutu, Ministar Kula da Harkokin Karamoja da dan uwanta Michael Naboya Kitutu bisa damfarar gwamnati.

  • Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON
  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda ta bayyana cewa ana tuhumar ‘yan uwan biyu da hada baki a damfarar gwamnati wajen sama da fadi da kayan da aka sayo don amfanin mutane marasa galihu a yankin Karamoja.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta kara da cewa an tsare ministar a kurkuku har nan da ranar 12 ga Afrilu.

A ranar Alhamis ne dai Minista Mary Goretti Kitutu da dan uwanta suka gurfana a gaban Kotun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda.

Labarai Masu Nasaba

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

An sayo kwanukan rufin don amfani da su wajen gina gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja, yankin da ke fama da rashin ci gaba, kuma yake fama da matsaloli a Arewa Maso Yammacin Uganda kusa da iyakar kasashen Kenya da Sudan ta Kudu.

Wannan abun kunya ya janyo ce-ce-ku-ce da kokawar jama’a da dama a kasar da cin hanci da rashawa suka yi wa gwamnatinta katutu.

Abu ne da ba a saba gani ba na gurfanar da babban mai rike da mukamin siyasa saboda zargin cin hanci da rashawa, kuma Kitutu ce jami’a mafi girman mukami da aka gurfanar a gaban kotu a ‘yan shekarun nan.

Abu mai kama da wannan da ya faru shi ne na 2007, lokacin da aka tuhumi wasu jami’an gwamnati biyu; Jim Muhwezi da Mike Mukula da sama da fadin miliyoyin daloli na bayar da agaji.

Madugun ‘yan adawar Uganda Bobi Wine ya ce tuhumar Kitutu ‘Da walakin ne’, ya kuma zargi gwamnatin Yoweri Museveni da zama mafi muni wajen aikata cin hanci da rashawa.

Mawakin da ya zama dan takarar shugaban kasa ya ce “Kamata ya yi dukkan mambobin gwamnatin Museveni da shi kansa su kasance a cikin kurkuku saboda cin hanci da rashawa”.

Ya kara da cewa “ba za mu yi murnar tuhuma kan kwanon rufi ba a lokacin da ake almabazzaranci da biliyoyin daloli.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MinistaUgandaZargin Sata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tinubu Na Son Dawo Da Sanusi A Matsayin Gwamnan CBN

Next Post

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

Related

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

5 days ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

1 week ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

2 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

2 weeks ago
Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Birtaniya, Faransa, Da Jamus Da Gazawa Kan Yarjejeniyar Nukiliyar 2015

3 weeks ago
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu
Kasashen Ketare

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

4 weeks ago
Next Post
Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.