ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Minista A Uganda Saboda Satar Kwanon Rufi

by Sadiq
3 years ago
Uganda

An daure Ministar gwamnatin Uganda a kurkuku a lamarin da ba a saba gani na rashawa da ya shafi manyan jami’ai, inda ake zarginta da sama da fadi da kwanon rufi da aka tanada don gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja na Arewacin kasar.

An tuhumi Mary Goretti Kitutu, Ministar Kula da Harkokin Karamoja da dan uwanta Michael Naboya Kitutu bisa damfarar gwamnati.

  • Hajjin 2023: Miliyan 3 Kowane Maniyyaci Zai Biya A Bana —NAHCON
  • An Samu Tsohuwar Hedimasta Da Laifin Yi Wa Dalibai Fyade

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda ta bayyana cewa ana tuhumar ‘yan uwan biyu da hada baki a damfarar gwamnati wajen sama da fadi da kayan da aka sayo don amfanin mutane marasa galihu a yankin Karamoja.

ADVERTISEMENT

Sanarwar da hukumar ta fitar ta kara da cewa an tsare ministar a kurkuku har nan da ranar 12 ga Afrilu.

A ranar Alhamis ne dai Minista Mary Goretti Kitutu da dan uwanta suka gurfana a gaban Kotun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Uganda.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

An sayo kwanukan rufin don amfani da su wajen gina gidajen masu karamin karfi a yankin Karamoja, yankin da ke fama da rashin ci gaba, kuma yake fama da matsaloli a Arewa Maso Yammacin Uganda kusa da iyakar kasashen Kenya da Sudan ta Kudu.

Wannan abun kunya ya janyo ce-ce-ku-ce da kokawar jama’a da dama a kasar da cin hanci da rashawa suka yi wa gwamnatinta katutu.

Abu ne da ba a saba gani ba na gurfanar da babban mai rike da mukamin siyasa saboda zargin cin hanci da rashawa, kuma Kitutu ce jami’a mafi girman mukami da aka gurfanar a gaban kotu a ‘yan shekarun nan.

Abu mai kama da wannan da ya faru shi ne na 2007, lokacin da aka tuhumi wasu jami’an gwamnati biyu; Jim Muhwezi da Mike Mukula da sama da fadin miliyoyin daloli na bayar da agaji.

Madugun ‘yan adawar Uganda Bobi Wine ya ce tuhumar Kitutu ‘Da walakin ne’, ya kuma zargi gwamnatin Yoweri Museveni da zama mafi muni wajen aikata cin hanci da rashawa.

Mawakin da ya zama dan takarar shugaban kasa ya ce “Kamata ya yi dukkan mambobin gwamnatin Museveni da shi kansa su kasance a cikin kurkuku saboda cin hanci da rashawa”.

Ya kara da cewa “ba za mu yi murnar tuhuma kan kwanon rufi ba a lokacin da ake almabazzaranci da biliyoyin daloli.”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

Kakakin Ofishin Jakadancin Sin Dake Amurka Ya Soki Lamirin Ganawar Tsai Ing-wen Da Kakakin Majalissar Wakilan Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.