• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

by Abubakar Sulaiman
3 hours ago
in Ilimi
0
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar wasu ɗalibai biyu na Makarantar Kwalejin Sakandare ta Gwamnati da ke Bichi, biyo bayan wani hari da wasu ɗalibai suka kai musu a cikin harabar makarantar.

Ɗaliban da suka rasu, Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, an ce an kai musu hari da wani abu mai kaifi da ake kira ‘Gwale-Gwale’, wanda wasu tsofaffin ɗalibai suka yi amfani da shi bayan da suka zargesu da aikata wani laifi da ba a bayyana ba, kuma suka ɗauki doka a hannunsu.

  • VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Wayar da Kan Jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar ranar Talata, 16 ga Yuli, 2025.

Sanarwar ta ce Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dr. Ali Haruna Makoɗa, ta bakin Babban Sakataren Ma’aikatar, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ya bayar da umarnin gudanar da bincike na gaskiya da adalci don gano haƙiƙanin abin da ya faru.

Babban Sakataren wanda ya kai ziyara makarantar, ya shawarci ɗalibai da su guji ɗaukar doka a hannunsu. “Ya kamata ku riƙa kai korafe-korafenku ga hukumomin makaranta domin ɗaukar matakin da ya dace,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Ya ƙara da cewa, “Muna mika ta’aziyyarmu ga iyalan da lamarin ya rutsa da su, tare da addu’ar Allah ya ba wa marigayyu Aljannatul Firdaus.”

Ƙin jin daɗin iyalan ya fito fili, inda Malam Ibrahim Yusuf Dungurawa, dangin marigayi Umar, ya bayyana yadda suka firgita da jin labarin mutuwar ɗansu, yana mai roƙon gwamnati da ta tabbatar da adalci. Haka zalika, Malam Idris Garba Tofawa, mahaifin marigayi Hamza, ya bayyana lamarin a matsayin ƙaddara daga Allah, amma ya bukaci hukuma ta ɗauki mataki cikin gaggawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kanoStudent
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Next Post

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Related

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)
Ilimi

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

4 days ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

2 weeks ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

3 weeks ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

3 weeks ago
Next Post
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

Kasar Sin Na Inganta Samun Nasara Ga Kowane Bangare A Fannin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki A Duniya

July 16, 2025
Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

Afrika Ta Zama Kasuwar Sayar Da Man Fetur Mara Inganci – Dangote

July 16, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

Xi Jinping Ya Mika Sakon Ta’aziyya Zuwa Ga Takwaransa Na Najeriya Bisa Rasuwar Muhammadu Buhari

July 16, 2025
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

July 16, 2025
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

July 16, 2025
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

July 16, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.