• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A lokacin da ake shirin kaddamar da taron makomar dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, an gudanar da wani biki mai taken “Makamashi na nan gaba” a birnin New York na kasar Amurka, a ranar 21 ga wata.

 

Kasashen da suka halarci bikin sun fitar da “Sanarwar makamashi na nan gaba”, da nufin inganta mu’ammala, da hadin gwiwa a fannin makamashi tsakanin mabambantan kasashe, tare da sa kaimi ga sauyawar tsare-tsaren makamashin duniya, da neman samun ci gaba mai dorewa ta fuskar harkar makamashi.

  • PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara
  • Kotu Ta Ba Da Belin Mawaki P Diddy Mai Safarar Mata

Hukumar hadin gwiwar kasashen duniya a fannin makamashi ta yanar gizo ta Internet, wadda kasar Sin ta kaddamar da aikin kafa ta, da kuma ofishin tsara dabaru na neman ci gaba mai dorewa na MDD ne suka karbi bakuncin bikin, inda sama da baki 200 daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30 suka halarci bikin.

 

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

A wajen bikin, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Fu Cong, ya bayyana a cikin jawabinsa cewa, yadda za a gina duniya mai tsafta da kyan gani, da tabbatar da makomar dan Adam mai kyau, wani babban batu ne da ke bukatar tunanin daukacin gamayyar kasa da kasa tare. Ya kamata al’ummomin kasa da kasa su karfafa hadin kai, da daukar matakan da suka dace wajen tinkarar kalubaloli, irinsu tsanantar sauyin yanayin duniya, da yawan aukuwar bala’o’i a kai a kai.
Kaza lika a sa kaimi ga daidaita makamashi cikin adalci, da gaggauta aiwatar da manufofin neman ci gaba mai dorewa.

 

Jami’in na Sin ya yi bayani kan nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin raya kasa da kare muhalli, a cikin ‘yan shekarun nan, inda ya yi nuni da cewa, kasar Sin ita ce kasar dake kan gaba wajen sauya tsarin raya tattalin arziki zuwa nau’in kare muhallin halittu, mai sa kaimi ga hadin gwiwar kasa da kasa a fannin daidaita makamashi, kana mai ba da gudummawa ga harkokin kula da makamashi da aikin kyautata yanayin duniya, yayin da kokarin kare muhalli ke zama tushe ga tsarin zamanantarwa na kasar Sin.

 

A nasa jawabin, manzon musamman na babban magatakardan MDD kan ayyukan daidaita yanayi Selwyn Hart, ya yabawa kasar Sin bisa gagarumar gudummawar da ta bayar a fannin raya tattalin arzikin duniya, tare da tabbatar da ingancin muhallin halittun duniya. Har ila yau, ya jaddada wajibcin mai da hankali kan maganar adalci yayin da ake sauya salon makamashi zuwa mai tsabta a duniya.

A cewarsa, a halin yanzu, yawancin jarin da ake zubawa a bangaren makamashi mai tsabta a kasashe masu sukuni suke, yayin da kasashe masu tasowa da dama suka kasa samun isashen jari. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara

Next Post

Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

6 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

9 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

10 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

1 day ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.