• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A lokacin da ake shirin kaddamar da taron makomar dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, an gudanar da wani biki mai taken “Makamashi na nan gaba” a birnin New York na kasar Amurka, a ranar 21 ga wata.

 

Kasashen da suka halarci bikin sun fitar da “Sanarwar makamashi na nan gaba”, da nufin inganta mu’ammala, da hadin gwiwa a fannin makamashi tsakanin mabambantan kasashe, tare da sa kaimi ga sauyawar tsare-tsaren makamashin duniya, da neman samun ci gaba mai dorewa ta fuskar harkar makamashi.

  • PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara
  • Kotu Ta Ba Da Belin Mawaki P Diddy Mai Safarar Mata

Hukumar hadin gwiwar kasashen duniya a fannin makamashi ta yanar gizo ta Internet, wadda kasar Sin ta kaddamar da aikin kafa ta, da kuma ofishin tsara dabaru na neman ci gaba mai dorewa na MDD ne suka karbi bakuncin bikin, inda sama da baki 200 daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 30 suka halarci bikin.

 

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

A wajen bikin, zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Fu Cong, ya bayyana a cikin jawabinsa cewa, yadda za a gina duniya mai tsafta da kyan gani, da tabbatar da makomar dan Adam mai kyau, wani babban batu ne da ke bukatar tunanin daukacin gamayyar kasa da kasa tare. Ya kamata al’ummomin kasa da kasa su karfafa hadin kai, da daukar matakan da suka dace wajen tinkarar kalubaloli, irinsu tsanantar sauyin yanayin duniya, da yawan aukuwar bala’o’i a kai a kai.
Kaza lika a sa kaimi ga daidaita makamashi cikin adalci, da gaggauta aiwatar da manufofin neman ci gaba mai dorewa.

 

Jami’in na Sin ya yi bayani kan nasarorin da kasar Sin ta samu a fannin raya kasa da kare muhalli, a cikin ‘yan shekarun nan, inda ya yi nuni da cewa, kasar Sin ita ce kasar dake kan gaba wajen sauya tsarin raya tattalin arziki zuwa nau’in kare muhallin halittu, mai sa kaimi ga hadin gwiwar kasa da kasa a fannin daidaita makamashi, kana mai ba da gudummawa ga harkokin kula da makamashi da aikin kyautata yanayin duniya, yayin da kokarin kare muhalli ke zama tushe ga tsarin zamanantarwa na kasar Sin.

 

A nasa jawabin, manzon musamman na babban magatakardan MDD kan ayyukan daidaita yanayi Selwyn Hart, ya yabawa kasar Sin bisa gagarumar gudummawar da ta bayar a fannin raya tattalin arzikin duniya, tare da tabbatar da ingancin muhallin halittun duniya. Har ila yau, ya jaddada wajibcin mai da hankali kan maganar adalci yayin da ake sauya salon makamashi zuwa mai tsabta a duniya.

A cewarsa, a halin yanzu, yawancin jarin da ake zubawa a bangaren makamashi mai tsabta a kasashe masu sukuni suke, yayin da kasashe masu tasowa da dama suka kasa samun isashen jari. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara

Next Post

Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

2 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

3 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

4 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

5 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

7 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.