• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

by Abubakar Abba
2 years ago
Makiyaya

An shirya taron bita na kwana daya kan yadda fulani makiyaya za su rika shuka ciyawa a Jihar Kaduna, domin ciyar da shanu da sauran dabbobinsu tare kuma da bunkasa kasuwancinta (ciyawar), tuni dai aka ware musu kadadar da za su fara shuka wannan ciyawa.

Haka zalika, matan fulani makiyayan kuma za a ba su shanu domin su fara samar da wadatacciyar madara a fadin jihar da kuma kasa baki-daya.

  • Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa
  • Sabon Salon ‘Yan Bindiga Na Sace Daliban Jami’a Mata…

Bugu da kari, an yi hakan ne domin samar musu da aikin yi da kuma rage rikicin da ke afkuwa a tsakanin makiyayan da monoma tare kuma da nufin mayar da ‘ya’yan fulani makarantar boko, su samu ilimin zamani.

Kungiyoyin fulani makiyaya biyu masu samar da madara wadanda suka fito daga Kananan Hukumomin Kubau da Chikun da ke Jihar Kaduna ne suka amfana da wannan shiri.

Har ila yau, shirin na daya daga cikin kokarin da take yi na bunkasa tattalin arzikin fulani makiyaya. Cibiyar bunkasa samar da madarar shanu (MBCF), karkashin shirin bunkasa sama wa matasa aikin yi ta hanyar noma da kiwo, wadda kungiyar ECOWAS ta dauki nauyi da wayar da kai.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Da take yin nata jawabin a wajen taron, Jami’ar Shirin Dakta Bilkisu Yusuf ta ce, an samar wannan da shiri ne domin rage yawan matasa marasa aikin yi a tsakanin fulani makiyaya da kuma tallafawa matansu.

Ta kara da cewa, shirin zai bai wa matasa makiyaya dama a kan yadda za su noma ciyawar shanu, a yayin kuma da za a bai wa matan makiyayan shanu; domin samar da wadatacciyar madara.

Bilkisu ta karfafawa matan guiwa kan su bai wa shirin goyon baya, musamman ganin yadda aka samar da shi domin tallafa wa rayuwarsu.

A karshe, wadanda suka amfana da wannan bita, sun yaba wa cibiyar bisa namijin kokarin da take yi na inganta rayuwa tare da alkawarin bayar da goyon baya, domin samun nasarar shirin a koda-yaushe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Masana Sun Bayar Da Mafita Kan Yadda Za A Samu Zaman Lafiya A Duniya

Masana Sun Bayar Da Mafita Kan Yadda Za A Samu Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.