ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar Makala Wa Mota Tukunyar Gas A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gas

Kwamitin albarkatun Gas na fadar shugaban kasa ya kaddamar da cibiyar dake ababen hawa daga amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a jihar Kaduna (CNG) a wani mataki na gwamnatin tarayya na rage wa jama’a wahalhalun da ake ciki sakamakon janye tallafin mai.

Da yake kaddamar da cibiyar a karshen mako, shugaban kwamitin CNG na fadar shugaban kasar, Zacch Adedeji, ya ce, cibiyar dake motocin ta CNG, an tsara ne domin canza tsarin amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a motoci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karfafa Shirin Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas
  • An Fitar Da Rahoton Yadda Kamfanonin Sin Ke Sauke Nauyin Al’umma A Afrika

Adedeji ya kara da cewa, cibiyar wata alama ce ta kawo gagarumin sauyi da sauki ga bangaren makamaci.

ADVERTISEMENT

Ya ce, (Wannan gagarumin sauyi ba kawai ma zai rage kudin kashe ga masu mallakin motoci ba ne, zai kuma taimaka sosai wajen rage iskar carbon.

“A yau, mun cimma wani nasara, samar da tsari mafi inganci da sauki da jama’a za su iya amfani da shi. Dukka wannan na cikin manufar gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu na farfado da kyakkyawar fata a bangaren bunkasa harkokin kere-kere da kiyaye muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

“Cibiyar dake motoci daga mai zuwa gas na cikin yunkurinmu na kawo mafiya ga bangaren makamaci da zai taimaka wa cigaba mai zuwa. Muna sane da cewa samar da sauki ga jama’a na daga cikin muhimmin abun bukata. Kuma CNG shi ne mafitar. Zai rage wa jama’a kashe kudade kamar yadda aka saba na sayen mai domin amfani yau da gobe.”

Shi ma da yake nasa jawabin, daraktan shirye-shirye na P-CNGi, Michael Oluwagbemi, ya ce, shirin CNG, na da kariya sosai kuma akwai saukin da ‘yan Nijeriya za su iya amfani da shi, kana zai bayar da dama wajen tsaftace muhalli, rage kashe kudade da kuma kula da lafiyar muhalli hadi da janyo mafita ga bangaren makamashi.

“Yana da kyau mu tuna cewa wannan cibiyar ba kawai ga Kaduna ba ce; ana maganar kasa ne baki daya da kuma duniya da ke bukatar kawo sauyi wajen kiyaye tsaftar muhalli da samar da sauki a bangaren makamashi.

“A yau mun tsaya kan tubalin kafa tarihi a jihar Kaduna, tare da manufar samar da makamashi mai daurewa cikin sauki, kuma da jama’a za su iya runguma cikin sauki da inganci.

“Wannan kaddamarwar ba kawai bikin bude cibiyar musaya ta CNG ba ce, a’a wani asasi ne na ganin an kawo gagarumin cigaba da zai bayar da dama a kaddamar da irin wannan cibiyar a jihohin Legas da Abuja,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Next Post
Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.