• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar Makala Wa Mota Tukunyar Gas A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin albarkatun Gas na fadar shugaban kasa ya kaddamar da cibiyar dake ababen hawa daga amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a jihar Kaduna (CNG) a wani mataki na gwamnatin tarayya na rage wa jama’a wahalhalun da ake ciki sakamakon janye tallafin mai.

Da yake kaddamar da cibiyar a karshen mako, shugaban kwamitin CNG na fadar shugaban kasar, Zacch Adedeji, ya ce, cibiyar dake motocin ta CNG, an tsara ne domin canza tsarin amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a motoci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karfafa Shirin Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas
  • An Fitar Da Rahoton Yadda Kamfanonin Sin Ke Sauke Nauyin Al’umma A Afrika

Adedeji ya kara da cewa, cibiyar wata alama ce ta kawo gagarumin sauyi da sauki ga bangaren makamaci.

Ya ce, (Wannan gagarumin sauyi ba kawai ma zai rage kudin kashe ga masu mallakin motoci ba ne, zai kuma taimaka sosai wajen rage iskar carbon.

“A yau, mun cimma wani nasara, samar da tsari mafi inganci da sauki da jama’a za su iya amfani da shi. Dukka wannan na cikin manufar gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu na farfado da kyakkyawar fata a bangaren bunkasa harkokin kere-kere da kiyaye muhalli.

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

“Cibiyar dake motoci daga mai zuwa gas na cikin yunkurinmu na kawo mafiya ga bangaren makamaci da zai taimaka wa cigaba mai zuwa. Muna sane da cewa samar da sauki ga jama’a na daga cikin muhimmin abun bukata. Kuma CNG shi ne mafitar. Zai rage wa jama’a kashe kudade kamar yadda aka saba na sayen mai domin amfani yau da gobe.”

Shi ma da yake nasa jawabin, daraktan shirye-shirye na P-CNGi, Michael Oluwagbemi, ya ce, shirin CNG, na da kariya sosai kuma akwai saukin da ‘yan Nijeriya za su iya amfani da shi, kana zai bayar da dama wajen tsaftace muhalli, rage kashe kudade da kuma kula da lafiyar muhalli hadi da janyo mafita ga bangaren makamashi.

“Yana da kyau mu tuna cewa wannan cibiyar ba kawai ga Kaduna ba ce; ana maganar kasa ne baki daya da kuma duniya da ke bukatar kawo sauyi wajen kiyaye tsaftar muhalli da samar da sauki a bangaren makamashi.

“A yau mun tsaya kan tubalin kafa tarihi a jihar Kaduna, tare da manufar samar da makamashi mai daurewa cikin sauki, kuma da jama’a za su iya runguma cikin sauki da inganci.

“Wannan kaddamarwar ba kawai bikin bude cibiyar musaya ta CNG ba ce, a’a wani asasi ne na ganin an kawo gagarumin cigaba da zai bayar da dama a kaddamar da irin wannan cibiyar a jihohin Legas da Abuja,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CNGKadunaLNG
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwararru Sun Bukaci Gwamnati Ta Zuba Jari A Fasahar Harkokin Sufurin Jirgin Ruwa

Next Post

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

5 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

5 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

6 hours ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

7 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

8 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

9 hours ago
Next Post
Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.