ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Cibiyar Makala Wa Mota Tukunyar Gas A Kaduna

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gas

Kwamitin albarkatun Gas na fadar shugaban kasa ya kaddamar da cibiyar dake ababen hawa daga amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a jihar Kaduna (CNG) a wani mataki na gwamnatin tarayya na rage wa jama’a wahalhalun da ake ciki sakamakon janye tallafin mai.

Da yake kaddamar da cibiyar a karshen mako, shugaban kwamitin CNG na fadar shugaban kasar, Zacch Adedeji, ya ce, cibiyar dake motocin ta CNG, an tsara ne domin canza tsarin amfani da man fetur zuwa amfani da iskar gas a motoci.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Karfafa Shirin Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas
  • An Fitar Da Rahoton Yadda Kamfanonin Sin Ke Sauke Nauyin Al’umma A Afrika

Adedeji ya kara da cewa, cibiyar wata alama ce ta kawo gagarumin sauyi da sauki ga bangaren makamaci.

ADVERTISEMENT

Ya ce, (Wannan gagarumin sauyi ba kawai ma zai rage kudin kashe ga masu mallakin motoci ba ne, zai kuma taimaka sosai wajen rage iskar carbon.

“A yau, mun cimma wani nasara, samar da tsari mafi inganci da sauki da jama’a za su iya amfani da shi. Dukka wannan na cikin manufar gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu na farfado da kyakkyawar fata a bangaren bunkasa harkokin kere-kere da kiyaye muhalli.

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

“Cibiyar dake motoci daga mai zuwa gas na cikin yunkurinmu na kawo mafiya ga bangaren makamaci da zai taimaka wa cigaba mai zuwa. Muna sane da cewa samar da sauki ga jama’a na daga cikin muhimmin abun bukata. Kuma CNG shi ne mafitar. Zai rage wa jama’a kashe kudade kamar yadda aka saba na sayen mai domin amfani yau da gobe.”

Shi ma da yake nasa jawabin, daraktan shirye-shirye na P-CNGi, Michael Oluwagbemi, ya ce, shirin CNG, na da kariya sosai kuma akwai saukin da ‘yan Nijeriya za su iya amfani da shi, kana zai bayar da dama wajen tsaftace muhalli, rage kashe kudade da kuma kula da lafiyar muhalli hadi da janyo mafita ga bangaren makamashi.

“Yana da kyau mu tuna cewa wannan cibiyar ba kawai ga Kaduna ba ce; ana maganar kasa ne baki daya da kuma duniya da ke bukatar kawo sauyi wajen kiyaye tsaftar muhalli da samar da sauki a bangaren makamashi.

“A yau mun tsaya kan tubalin kafa tarihi a jihar Kaduna, tare da manufar samar da makamashi mai daurewa cikin sauki, kuma da jama’a za su iya runguma cikin sauki da inganci.

“Wannan kaddamarwar ba kawai bikin bude cibiyar musaya ta CNG ba ce, a’a wani asasi ne na ganin an kawo gagarumin cigaba da zai bayar da dama a kaddamar da irin wannan cibiyar a jihohin Legas da Abuja,” ya shaida.

Gas
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
Labarai

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
Labarai

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC
Labarai

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Next Post
Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.