• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
in Labarai
0
An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

An bayyana shirin Gwamnati Na Kano CARRES da cewa shi ne shirin da yafi sauran shirye shiryen da ake bijiro dasu da sunan tallafin saukakawa jama’a radadin matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita tun bayan faruwar Annobar Korona wadda tayi sanadin durkushewar tatalin jama’a.

Shugaban Hukumar Kano CARES na Jihar Kano Alhaji Rufa’I ne yabayyana haka alokacin da yake zagawa da babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir alokacin shirin da ake na kaddamar da tallafin kayan Noma ga daruruwan matasa maza da mata a Jihar Kano.

  • Tinubu Ya Kori Shugaban Hukumar NASENI Bayan Wata 3 Da Nadinsa
  • Rage Radadin Cire Tallafi: Gwamnati Ta Baiwa  Kowacce Jiha Naira Biliyan Biyu A Kashin Farko

Alhaji Rufa’I ya shaidawa Babban sakataren Ma’aikatar gonan na jIhar Kano cewar wannan hukuma ta himmatu kamar yadda aka bata cikin kudin tsare tsaren wannan hukuma na samar da tallafi kamar bayar da injunan nika, injin malkade, injin ban ruwa mai amfani da hasken rana, kiwon Kaji, samar da hanyoyi a karkara da kuma gina wuraren kewayawa a kasuwanni da wuraren taruwar al’umma.

Hakazalika shugaban hukumar ta Kano CARES  ya bayyanawa mahalarta taron irin yadda majalisar mahaddata alkur’ani suma suka shigo cikin tsarin, musamman ganin suna da kyakkyawan shirin rage kwararar almajirai daga kauyuka zuwa manyan birane tare da kokarin magance matsalar barace barace wadda a halin ke neman zama wata barazana a jihar Kano, don haka sai ya tabbatar da cewa yanzu haka shirye shirye sunyi nisa na sake samar da wani rukunin al’umma da suma ake fatan zasu rabauta da wannan tallafi da Gwamnatin Kano ke saukewa al’ummarta.

Da yake jawabi alokacin da yake ganewa idonsa irin kayayyakin da hukumar ta samar domin rabawa al’umma musamman abinda ya shafi noma, kiwo da sana’o’in dogaro da kai, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana farin cikinsa tare da jinjinawa kokarin wannan hukuma wadda yace babu shakka ya fahimci yadda jama’a ke alfahari da ayyukan wannan hukuma ke nuni da kyakkyawan alhairan da ke kunshe cikin manufofi da aikace aikacen hukumar ta Kano CARES.

Shima da yake duba kayayyakin da hukumar Kano CARES ta tanada domin ci gaba da rabawa jama’a, babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir ya nuna gamsuwa da irin kalaman da yaji daga bakin wadanda suka amfana da alhairan wannan hukuma ta Kano CARES, musamman kan batan smaar da hanyoyi a karkara, inda wasu da suka amfana daga Kananan Hukumomi Gazawa da Kura suka bayyana farin cikin al’umarsu bis aaikin hanya da wannan hukuma ta shimfada masu a yankunansu.

Alhaji Salisu Tahir ya jinjinawa kokarin shugabannin hukuma tare da rokonsu da su kara himma wajen sauke nauyin da aka dora masu, sannan kuma ya bukaci wadanda suka amfana da wadanann tallafi iri daban daban da suyi kyakkyawan amfani dashi, domin ganin nan gaba kadan suma sun zama suna cikin wadanda da za su taimaka wa sauran al’umma. A karshe ya yi addu’ar Allah ya sawa damunar mu albarka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

Next Post

Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

5 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

8 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

8 hours ago
Noma
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

10 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

12 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

12 hours ago
Next Post
Gwamnan Kaduna

Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Noma

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.