• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ribadu

Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaron Kasa (NSA), Nuhu Ribadu, ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu a harin da aka kai wa shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya, Joe Ajero.

Ofishin na NSA, wanda ya nuna damuwasa kan faruwar lamarin inda ya ce tun daga lokacin abin ya faru aka fara bincike akai.

  • Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.35
  • Haaland Ya Samu Rauni Yayin Buga Wasan Sada Zumunta

Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da jamiin yada labarai na mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Zakari Mijinyawa ya fitar.

A wani bangare, sanarwar ta ce, Mai bai wa shugaban kasa shawarar ya bukaci kungiyar kwadago ta janye yajin aikin, domin ya yi Allah-wadai da harin da aka kai wa shugaban na NLC, ya ce an fara kama wddanda ake zargi da kai harin gami da ci gaba da bincike.

Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro ya damu da ayyana yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka yi a fadin kasar. Ofishin na NSA ya damu musamman game da illolin yajin aikin ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma illar da ke iya haifarwa ga tsaron tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take ofishin na NSA ya shiga tsakani domin samun labarin halin da shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya Joseph Ajaero ya tsinci kansa a Garin Owerri na Jihar Imo. NSA ya yi bakin cikin faruwar lamarin tare da yin Allah-wadai da lamarin baki daya domin ya saba wa doka da kaidojin yancin fadin albarkacin baki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa suka yi. Gwamnatin Tarayya ba za ta taba lamuntar irin wannan mummunan aiki ba.

NSA ya bayar da tabbacin cewa za a bayyana sakamakon binciken, inda ya yi kira ga kungiyoyin da su janye yajin aikin.

Kamar yadda lamarin ya faru, an umurci hukumomin da suka dace da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu. Ci gaban da ake samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da suke hannu a lamarin. Za mu fito da sahihan bayanai game da sakamakon binciken da zarar an kammala shi.

Sanarwar ta kara da cewa, Gwamnatin tarayya ta ofishin NSA, tana kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, su bari a ci gaba da tattaunawa har a cimma matsaya, in ji sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 – Musa Iliyasu Ga Abba

Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 - Musa Iliyasu Ga Abba

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.