• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaron Kasa (NSA), Nuhu Ribadu, ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu a harin da aka kai wa shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya, Joe Ajero.

Ofishin na NSA, wanda ya nuna damuwasa kan faruwar lamarin inda ya ce tun daga lokacin abin ya faru aka fara bincike akai.

  • Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.35
  • Haaland Ya Samu Rauni Yayin Buga Wasan Sada Zumunta

Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da jamiin yada labarai na mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Zakari Mijinyawa ya fitar.

A wani bangare, sanarwar ta ce, Mai bai wa shugaban kasa shawarar ya bukaci kungiyar kwadago ta janye yajin aikin, domin ya yi Allah-wadai da harin da aka kai wa shugaban na NLC, ya ce an fara kama wddanda ake zargi da kai harin gami da ci gaba da bincike.

Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro ya damu da ayyana yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka yi a fadin kasar. Ofishin na NSA ya damu musamman game da illolin yajin aikin ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma illar da ke iya haifarwa ga tsaron tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take ofishin na NSA ya shiga tsakani domin samun labarin halin da shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya Joseph Ajaero ya tsinci kansa a Garin Owerri na Jihar Imo. NSA ya yi bakin cikin faruwar lamarin tare da yin Allah-wadai da lamarin baki daya domin ya saba wa doka da kaidojin yancin fadin albarkacin baki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa suka yi. Gwamnatin Tarayya ba za ta taba lamuntar irin wannan mummunan aiki ba.

NSA ya bayar da tabbacin cewa za a bayyana sakamakon binciken, inda ya yi kira ga kungiyoyin da su janye yajin aikin.

Kamar yadda lamarin ya faru, an umurci hukumomin da suka dace da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu. Ci gaban da ake samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da suke hannu a lamarin. Za mu fito da sahihan bayanai game da sakamakon binciken da zarar an kammala shi.

Sanarwar ta kara da cewa, Gwamnatin tarayya ta ofishin NSA, tana kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, su bari a ci gaba da tattaunawa har a cimma matsaya, in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Joe AjaeroNlcNSATUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Saudiyya Sun Kulla Alakar Musayar Fasaha A Bangaren Mai

Next Post

Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 – Musa Iliyasu Ga Abba

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

2 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

4 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

9 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

11 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

12 hours ago
Next Post
Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 – Musa Iliyasu Ga Abba

Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 - Musa Iliyasu Ga Abba

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.