ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Ribadu

Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaron Kasa (NSA), Nuhu Ribadu, ya ce an kama wasu da ake zargi da hannu a harin da aka kai wa shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya, Joe Ajero.

Ofishin na NSA, wanda ya nuna damuwasa kan faruwar lamarin inda ya ce tun daga lokacin abin ya faru aka fara bincike akai.

  • Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.35
  • Haaland Ya Samu Rauni Yayin Buga Wasan Sada Zumunta

Ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da jamiin yada labarai na mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Zakari Mijinyawa ya fitar.

ADVERTISEMENT

A wani bangare, sanarwar ta ce, Mai bai wa shugaban kasa shawarar ya bukaci kungiyar kwadago ta janye yajin aikin, domin ya yi Allah-wadai da harin da aka kai wa shugaban na NLC, ya ce an fara kama wddanda ake zargi da kai harin gami da ci gaba da bincike.

Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro ya damu da ayyana yajin aikin da shugabannin kungiyoyin kwadagon karkashin jagorancin NLC da TUC suka yi a fadin kasar. Ofishin na NSA ya damu musamman game da illolin yajin aikin ga rayuwar talakawan Nijeriya da kuma illar da ke iya haifarwa ga tsaron tattalin arziki da sauran manyan muradun kasa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Kamar yadda shugabannin NLC suka shaida, nan take ofishin na NSA ya shiga tsakani domin samun labarin halin da shugaban kungiyar kwadago ta Nijeriya Joseph Ajaero ya tsinci kansa a Garin Owerri na Jihar Imo. NSA ya yi bakin cikin faruwar lamarin tare da yin Allah-wadai da lamarin baki daya domin ya saba wa doka da kaidojin yancin fadin albarkacin baki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa suka yi. Gwamnatin Tarayya ba za ta taba lamuntar irin wannan mummunan aiki ba.

NSA ya bayar da tabbacin cewa za a bayyana sakamakon binciken, inda ya yi kira ga kungiyoyin da su janye yajin aikin.

Kamar yadda lamarin ya faru, an umurci hukumomin da suka dace da su gudanar da cikakken bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda suka aikata laifin gaban kotu. Ci gaban da ake samu na nuni da cewa an riga an kama wasu da suke hannu a lamarin. Za mu fito da sahihan bayanai game da sakamakon binciken da zarar an kammala shi.

Sanarwar ta kara da cewa, Gwamnatin tarayya ta ofishin NSA, tana kira ga shugabannin kwadago da su janye yajin aikin da suke yi a halin yanzu, su bari a ci gaba da tattaunawa har a cimma matsaya, in ji sanarwar.

Ribadu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 – Musa Iliyasu Ga Abba

Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 - Musa Iliyasu Ga Abba

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.