• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Siyasa
0
An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gano wani yunkuri a cikin jam’iyyar adawa ta PDP na barin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Iliya Damagum ya ci gba da rike mukaminsa har na tsawon wa’adin Dakta Iyorchia Ayu ya kare a 2025.

Duk da cewa tun da farko an tsayar da taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, taron gwamnonin jam’iyyar PDP da suka gudanar a Bauchi a karshen mako sun nuna cewa a dage zaben zuwa wani lokaci a cikin watan Fabrairun 2025, domin samun damar jam’iyyar ta warware matsalarta na ciki gida.

  • Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora
  • Online Payday Loans In Conrad, Montana Mt From Direct Lenders

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida cewa matakin sauya shekar na kwamitin zartarwar nasara ce ga masu neman Damagum ya ci gaba da rike mukamin har zuwa karshen shekarar 2025.

Wata majiya ta ce tuni aka samu rabuwar kawuna, inda bangarori biyu suka kunno kai a cikin jam’iyyar PDP. Yayin da aka ce wani bangare wanda ya hada da wasu gwamnoni da masu ruwa da tsaki na kokarin ganin an tsawaita wa’adin zama a Damagum, dayan bangaren wanda kuma ya kunshi wasu gwamnoni da wasu masu fada ji na jam’iyyar suna aiki tukuru wajen ganin an zabi wani shugaban jam’iyya, wanda zai tabbatar da bin tsarin mulkin jam’iyyar kamar yadda aka saba a baya.

Damagum ya fito ne daga shiyyar arewa maso gabas, tun farko an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa reshen arewa kafin ya hau kujerar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, bayan tsige Dakta Iyorchia Ayu.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya nuna cewa dole ne wanda zai maye gurbin Ayu ya fito daga yanki da da shi, amma makirci ya mamaye jam’iyyar, wanda ya tabbatar da tsawaita jinkirin aiwatar da maye gurbin.

Wani shiri na samar da wanda zai maye gurbinsa daga arewa ta tsakiya ya ci karo da matsaloli bayan dage babban taron kwamitin zartarwa na jam’iyya da aka yi akai-akai. Taron na karshe da kwamitin zartarwa na jam’iyyar ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu, an sanya ranar 15 ga watan Agusta domin gudanar da zaben shugaban jam’iyyar karo na 99, amma an dage taron da farko zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, sannan zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, wanda a yanzu kungiyar gwamnonin na jam’iyyar ta kara dagawa.

Bincike ya nuna cewa yayin da masu neman maye gurbin Damagum ke neman wanda zai iya karbar ragamar mulki nan take, masu goyon bayan ci gaba da aikinsa a ofishin sun yi ta aiki a asirce kan yadda zai karasa sauran wa’adin Ayu, sannan kuma a sake zabensa a karo na biyu a 2025 don samun cikakken wa’adinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Yi Garambawul Da Bullo Da Sabon Ci Gaban Kasuwancin Fasahohin Zamani

Next Post

Ƙasurguman ‘Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

2 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

3 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

4 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Ƙasurguman 'Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.