• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025

byYusuf Shuaibu
10 months ago
PDP

An gano wani yunkuri a cikin jam’iyyar adawa ta PDP na barin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Iliya Damagum ya ci gba da rike mukaminsa har na tsawon wa’adin Dakta Iyorchia Ayu ya kare a 2025.

Duk da cewa tun da farko an tsayar da taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, taron gwamnonin jam’iyyar PDP da suka gudanar a Bauchi a karshen mako sun nuna cewa a dage zaben zuwa wani lokaci a cikin watan Fabrairun 2025, domin samun damar jam’iyyar ta warware matsalarta na ciki gida.

  • Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora
  • Online Payday Loans In Conrad, Montana Mt From Direct Lenders

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida cewa matakin sauya shekar na kwamitin zartarwar nasara ce ga masu neman Damagum ya ci gaba da rike mukamin har zuwa karshen shekarar 2025.

Wata majiya ta ce tuni aka samu rabuwar kawuna, inda bangarori biyu suka kunno kai a cikin jam’iyyar PDP. Yayin da aka ce wani bangare wanda ya hada da wasu gwamnoni da masu ruwa da tsaki na kokarin ganin an tsawaita wa’adin zama a Damagum, dayan bangaren wanda kuma ya kunshi wasu gwamnoni da wasu masu fada ji na jam’iyyar suna aiki tukuru wajen ganin an zabi wani shugaban jam’iyya, wanda zai tabbatar da bin tsarin mulkin jam’iyyar kamar yadda aka saba a baya.

Damagum ya fito ne daga shiyyar arewa maso gabas, tun farko an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa reshen arewa kafin ya hau kujerar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, bayan tsige Dakta Iyorchia Ayu.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya nuna cewa dole ne wanda zai maye gurbin Ayu ya fito daga yanki da da shi, amma makirci ya mamaye jam’iyyar, wanda ya tabbatar da tsawaita jinkirin aiwatar da maye gurbin.

Wani shiri na samar da wanda zai maye gurbinsa daga arewa ta tsakiya ya ci karo da matsaloli bayan dage babban taron kwamitin zartarwa na jam’iyya da aka yi akai-akai. Taron na karshe da kwamitin zartarwa na jam’iyyar ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu, an sanya ranar 15 ga watan Agusta domin gudanar da zaben shugaban jam’iyyar karo na 99, amma an dage taron da farko zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, sannan zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, wanda a yanzu kungiyar gwamnonin na jam’iyyar ta kara dagawa.

Bincike ya nuna cewa yayin da masu neman maye gurbin Damagum ke neman wanda zai iya karbar ragamar mulki nan take, masu goyon bayan ci gaba da aikinsa a ofishin sun yi ta aiki a asirce kan yadda zai karasa sauran wa’adin Ayu, sannan kuma a sake zabensa a karo na biyu a 2025 don samun cikakken wa’adinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Ƙasurguman 'Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version