• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi

by Umar Faruk and Sulaiman
1 year ago
Aliero

Wasu masu ababen hawa a Koko Besse, Jega da Birnin Kebbi sun yaba wa Sanata Muhammadu Adamu Aliero mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya kan gyaran gadar da ta ruguje da ta hada Arewa maso Yamma da Kudancin kasar nan.

 

Idan dai za a iya tunawa, gadar da ke tsakanin garuruwan Kuchi da Rara a kan babbar hanyar da ta hada jihohin Kebbi, Sokoto, da Neja ta rushe a ranar 29 ga watan Agusta.

  • ’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu
  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai

Ta ruguje ne a daren Lahadi sakamakon mamakon ruwan sama da ya addabi jihar Kebbi da sauran jihohin da ke makwabtaka da jihar kamar Sokoto, Zamfara da Neja.

 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

Sanata Aliero wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin sufurin kasa, ya gyara gadar da ta ruguje, wadda ta janyo wa masu ababen hawa da manoma da ke tuka titin wahala matuka bayan rugujewar ta.

 

Masu ababen hawa da manoman sun bayyana jin dadinsu tare da yabawa a hirarsu manema Labarai daban-daban a karamar hukumar Koko/Besse da Jega da Birnin kebbi.

 

Alhaji Yahaya Malami, direban ‘yan kasuwa, ya yabawa Sanata Aliero kan gyaran gadar da aka yi, ya ce kamar an maido da gadar kamar yadda take.

 

“Kafin gyaran gadar, mun fuskanci kalubale na tafiyar kan hanyar zuwa Kudancin kasar nan.

 

“Duk direban da zai je yankin Kudancin kasar nan sai ya bi Jega, sannan ya zarce zuwa kananan hukumomin Kalgo, Bunza, Suru, da Bagudo sannan ya koma hanyarsa ta yau da kullun a Koko-Basse don ci gaba da tafiya Kudancin kasar nan.

 

“Sakamakon tashin farashin man fetur, masu ababen hawa da fasinjoji sun fuskanci wahalhalu da yawa kafin su je yankin Kudancin kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kuma bukaci direbobin da su kara kaimi ga kokarin sanata da gwamnati na hana afkuwar hadurran mota ta hanyar samar da ingantattun hanyoyi ta hanyar gujewa wuce gona da iri da kuma cunkoso yayin tukun motocinsu a kan hanya.

 

“Gyaran gadar ya sauƙaƙa wahalhalun da muke fuskanta a cikin zirga-zirgar ababen hawa daga jihar Kebbi zuwa Yauri har zuwa Kudancin ƙasar nan.

 

“Mun yi tunanin cewa gadar da ta ruguje za ta dauki lokaci mai tsawo kafin a gyara ta, kuma yanzu an gyara ta.

 

“Mun yi farin ciki, kuma muna godiya ga Gwamnatin Tarayya da kuma Sanata Adamu Aleiro don ceton rayukanmu da na fasinjojinmu,” in ji shi.

 

Shi ma Malam Nura Abubakar ya bukaci masu ababen hawa da ke amfani da hanyar da su rika tuka mota cikin aminci da bin ka’idojin kiyaye hanya domin kare rayuka da dukiyoyi da ababen more rayuwa a yankin a yayin tafiya kan wannan babbar hanyar.

 

A nasa bangaren, Alhaji Tsoho Alaye-Jega, Magoya bayan Sanata Aleiro, ya yabawa Sanatan tare da yin kira ga jama’a da su yaba da kokarin Sanatan na samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummarsa a jihar.

 

“Wannan gadar hanyar gwamnatin tarayya ce, amma Sanata Muhammadu Adamu Aleiro ya dauki nauyin gyara ta saboda muhimmancinta na tattalin arziki ga jama’ar wanda ba na jihar Kebbi kadai ba, har ma daga jahohin Sakkwato, Zamfara da Neja da sauransu.

 

“Dole ne mu gode masa kan abin da ya yi a yanzu, da abin da yake yi wa mutanen jihar Kebbi.

 

“Wannan ya nuna cewa muna da wakili nagari mai wakiltar mazabarmu na Kebbi ta tsakiya, kuma muna kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi da shi,” inji shi.

 

Alhaji Alaye-Jega, ya yi kira ga dukkan magoya bayan Sanata Aliero na gundumar Kebbi ta tsakiya da kuma sauran masu biyayya a fadin jihar da su ci gaba da marawa Sanatan baya don ganin an samar da karin gajiyar dimokradiyya daga hannun Sanatan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.