• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi

by Umar Faruk and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu ababen hawa a Koko Besse, Jega da Birnin Kebbi sun yaba wa Sanata Muhammadu Adamu Aliero mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya kan gyaran gadar da ta ruguje da ta hada Arewa maso Yamma da Kudancin kasar nan.

 

Idan dai za a iya tunawa, gadar da ke tsakanin garuruwan Kuchi da Rara a kan babbar hanyar da ta hada jihohin Kebbi, Sokoto, da Neja ta rushe a ranar 29 ga watan Agusta.

  • ’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu
  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai

Ta ruguje ne a daren Lahadi sakamakon mamakon ruwan sama da ya addabi jihar Kebbi da sauran jihohin da ke makwabtaka da jihar kamar Sokoto, Zamfara da Neja.

 

Labarai Masu Nasaba

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Sanata Aliero wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin sufurin kasa, ya gyara gadar da ta ruguje, wadda ta janyo wa masu ababen hawa da manoma da ke tuka titin wahala matuka bayan rugujewar ta.

 

Masu ababen hawa da manoman sun bayyana jin dadinsu tare da yabawa a hirarsu manema Labarai daban-daban a karamar hukumar Koko/Besse da Jega da Birnin kebbi.

 

Alhaji Yahaya Malami, direban ‘yan kasuwa, ya yabawa Sanata Aliero kan gyaran gadar da aka yi, ya ce kamar an maido da gadar kamar yadda take.

 

“Kafin gyaran gadar, mun fuskanci kalubale na tafiyar kan hanyar zuwa Kudancin kasar nan.

 

“Duk direban da zai je yankin Kudancin kasar nan sai ya bi Jega, sannan ya zarce zuwa kananan hukumomin Kalgo, Bunza, Suru, da Bagudo sannan ya koma hanyarsa ta yau da kullun a Koko-Basse don ci gaba da tafiya Kudancin kasar nan.

 

“Sakamakon tashin farashin man fetur, masu ababen hawa da fasinjoji sun fuskanci wahalhalu da yawa kafin su je yankin Kudancin kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kuma bukaci direbobin da su kara kaimi ga kokarin sanata da gwamnati na hana afkuwar hadurran mota ta hanyar samar da ingantattun hanyoyi ta hanyar gujewa wuce gona da iri da kuma cunkoso yayin tukun motocinsu a kan hanya.

 

“Gyaran gadar ya sauƙaƙa wahalhalun da muke fuskanta a cikin zirga-zirgar ababen hawa daga jihar Kebbi zuwa Yauri har zuwa Kudancin ƙasar nan.

 

“Mun yi tunanin cewa gadar da ta ruguje za ta dauki lokaci mai tsawo kafin a gyara ta, kuma yanzu an gyara ta.

 

“Mun yi farin ciki, kuma muna godiya ga Gwamnatin Tarayya da kuma Sanata Adamu Aleiro don ceton rayukanmu da na fasinjojinmu,” in ji shi.

 

Shi ma Malam Nura Abubakar ya bukaci masu ababen hawa da ke amfani da hanyar da su rika tuka mota cikin aminci da bin ka’idojin kiyaye hanya domin kare rayuka da dukiyoyi da ababen more rayuwa a yankin a yayin tafiya kan wannan babbar hanyar.

 

A nasa bangaren, Alhaji Tsoho Alaye-Jega, Magoya bayan Sanata Aleiro, ya yabawa Sanatan tare da yin kira ga jama’a da su yaba da kokarin Sanatan na samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummarsa a jihar.

 

“Wannan gadar hanyar gwamnatin tarayya ce, amma Sanata Muhammadu Adamu Aleiro ya dauki nauyin gyara ta saboda muhimmancinta na tattalin arziki ga jama’ar wanda ba na jihar Kebbi kadai ba, har ma daga jahohin Sakkwato, Zamfara da Neja da sauransu.

 

“Dole ne mu gode masa kan abin da ya yi a yanzu, da abin da yake yi wa mutanen jihar Kebbi.

 

“Wannan ya nuna cewa muna da wakili nagari mai wakiltar mazabarmu na Kebbi ta tsakiya, kuma muna kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi da shi,” inji shi.

 

Alhaji Alaye-Jega, ya yi kira ga dukkan magoya bayan Sanata Aliero na gundumar Kebbi ta tsakiya da kuma sauran masu biyayya a fadin jihar da su ci gaba da marawa Sanatan baya don ganin an samar da karin gajiyar dimokradiyya daga hannun Sanatan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan More rayuwaKatsewar GadaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Related

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

1 hour ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

2 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

3 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

6 hours ago
Borno
Labarai

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

8 hours ago
Yajin aiki
Labarai

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

9 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

LABARAI MASU NASABA

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.