• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi

by Umar Faruk and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
An Yaba wa Sanata Aliero Kan Gyara Gadar Keɓɓe Da Ta Ruguje A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu ababen hawa a Koko Besse, Jega da Birnin Kebbi sun yaba wa Sanata Muhammadu Adamu Aliero mai wakiltar mazabar Kebbi ta tsakiya kan gyaran gadar da ta ruguje da ta hada Arewa maso Yamma da Kudancin kasar nan.

 

Idan dai za a iya tunawa, gadar da ke tsakanin garuruwan Kuchi da Rara a kan babbar hanyar da ta hada jihohin Kebbi, Sokoto, da Neja ta rushe a ranar 29 ga watan Agusta.

  • ’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu
  • An Bude Baje Kolin CIIE Karo Na 7 A Birnin Shanghai

Ta ruguje ne a daren Lahadi sakamakon mamakon ruwan sama da ya addabi jihar Kebbi da sauran jihohin da ke makwabtaka da jihar kamar Sokoto, Zamfara da Neja.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Sanata Aliero wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da harkokin sufurin kasa, ya gyara gadar da ta ruguje, wadda ta janyo wa masu ababen hawa da manoma da ke tuka titin wahala matuka bayan rugujewar ta.

 

Masu ababen hawa da manoman sun bayyana jin dadinsu tare da yabawa a hirarsu manema Labarai daban-daban a karamar hukumar Koko/Besse da Jega da Birnin kebbi.

 

Alhaji Yahaya Malami, direban ‘yan kasuwa, ya yabawa Sanata Aliero kan gyaran gadar da aka yi, ya ce kamar an maido da gadar kamar yadda take.

 

“Kafin gyaran gadar, mun fuskanci kalubale na tafiyar kan hanyar zuwa Kudancin kasar nan.

 

“Duk direban da zai je yankin Kudancin kasar nan sai ya bi Jega, sannan ya zarce zuwa kananan hukumomin Kalgo, Bunza, Suru, da Bagudo sannan ya koma hanyarsa ta yau da kullun a Koko-Basse don ci gaba da tafiya Kudancin kasar nan.

 

“Sakamakon tashin farashin man fetur, masu ababen hawa da fasinjoji sun fuskanci wahalhalu da yawa kafin su je yankin Kudancin kasar nan,” in ji shi.

 

Ya kuma bukaci direbobin da su kara kaimi ga kokarin sanata da gwamnati na hana afkuwar hadurran mota ta hanyar samar da ingantattun hanyoyi ta hanyar gujewa wuce gona da iri da kuma cunkoso yayin tukun motocinsu a kan hanya.

 

“Gyaran gadar ya sauƙaƙa wahalhalun da muke fuskanta a cikin zirga-zirgar ababen hawa daga jihar Kebbi zuwa Yauri har zuwa Kudancin ƙasar nan.

 

“Mun yi tunanin cewa gadar da ta ruguje za ta dauki lokaci mai tsawo kafin a gyara ta, kuma yanzu an gyara ta.

 

“Mun yi farin ciki, kuma muna godiya ga Gwamnatin Tarayya da kuma Sanata Adamu Aleiro don ceton rayukanmu da na fasinjojinmu,” in ji shi.

 

Shi ma Malam Nura Abubakar ya bukaci masu ababen hawa da ke amfani da hanyar da su rika tuka mota cikin aminci da bin ka’idojin kiyaye hanya domin kare rayuka da dukiyoyi da ababen more rayuwa a yankin a yayin tafiya kan wannan babbar hanyar.

 

A nasa bangaren, Alhaji Tsoho Alaye-Jega, Magoya bayan Sanata Aleiro, ya yabawa Sanatan tare da yin kira ga jama’a da su yaba da kokarin Sanatan na samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummarsa a jihar.

 

“Wannan gadar hanyar gwamnatin tarayya ce, amma Sanata Muhammadu Adamu Aleiro ya dauki nauyin gyara ta saboda muhimmancinta na tattalin arziki ga jama’ar wanda ba na jihar Kebbi kadai ba, har ma daga jahohin Sakkwato, Zamfara da Neja da sauransu.

 

“Dole ne mu gode masa kan abin da ya yi a yanzu, da abin da yake yi wa mutanen jihar Kebbi.

 

“Wannan ya nuna cewa muna da wakili nagari mai wakiltar mazabarmu na Kebbi ta tsakiya, kuma muna kira ga ‘yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi da shi,” inji shi.

 

Alhaji Alaye-Jega, ya yi kira ga dukkan magoya bayan Sanata Aliero na gundumar Kebbi ta tsakiya da kuma sauran masu biyayya a fadin jihar da su ci gaba da marawa Sanatan baya don ganin an samar da karin gajiyar dimokradiyya daga hannun Sanatan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ayyukan More rayuwaKatsewar GadaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Siyasar Amurka Na Bata Demokuradiyyar Kasarsu

Next Post

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Related

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

3 hours ago
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano
Labarai

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

4 hours ago
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 
Manyan Labarai

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

4 hours ago
Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

7 hours ago
Shettima
Labarai

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

7 hours ago
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 
Manyan Labarai

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

9 hours ago
Next Post
Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Lardin Hubei

LABARAI MASU NASABA

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

September 3, 2025
Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.