• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin jakadancin Sin dake Zimbabwe, ya gudanar da bikin cika shekaru 60 da fara tura tawagar jami’an lafiya na kasar Sin zuwa ketare, tare da maraba da tawaga ta 20 na jami’an lafiya da Sin ta tura kasar a ran 8 ga watan.

Haka kuma, bikin ya taya tawaga ta 19 ta jami’an lafiya ta kasar Sin, murnar kammala aikinsu na shekara 1 a kasar, cikin nasara.

Tun bayan da Sin ta tura tawaga ta farko ta jami’an lafiya zuwa kasar Algeria a 1963, kawo yanzu, ta tura jimilar jami’an lafiya 30,000, wadanda suka bada kulawar lafiya ga mutane miliyan 290 a kasashe da yankuna 76. Yanzu haka, tawagar jami’an lafiya na kasar Sin na aiki a birane 115 a kasashe 56 a fadin duniya.

Tun daga shekarar 1985 zuwa yanzu, kasar Sin ta tura tawagogin jami’an lafiya 20 zuwa kasar Zimbabwe. Kuma cikin shekarar da ta gabata, tawaga ta 19 ta yi aiki bisa hadin gwiwa da ma’aikatar lafiya ta kasar da sassa masu ruwa da tsaki, wajen samar da kiwon lafiya ga al’ummar Zimbabwe.

Da yake jawabi yayin bikin, mataimakin shugaban kasar Zimbabwe kuma ministan lafiya na kasar, Constantino Chiwenga, ya yaba da rawar da kasar da Sin da ma jami’an lafiyar suka taka wajen yaki da annobar COVID-19 a kasar. Yana mai cewa, kashin farko na alluran riga kafin cutar da ya shiga kasar a watan Fabrerun 2021, gudunmawa ce daga gwamnatin kasar Sin, lamarin da ya kaddamar da ganganmin riga kafi cikin nasara a kasar, inda zuwa yanzu ta yi wa kaso 60.8 na jama’arta riga kafi.

Labarai Masu Nasaba

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Sannan aka yi bikin mika aiki daga tawagar likitoci ta kasar Sin dake kasar Zimbabwe karo na 19 zuwa ta 20 a birnin Harare, inda mukaddashin jakadan Sin dake Zimbabwe Cheng Yan da mataimakin shugaban Zimbabwe kuma ministan kiwon lafiyar kasar Constantino Chiwenga suka halarci bikin.

A yayin bikin, a madadin gwamnatin Zimbabwe, minista Chiwenga ya ba da lambar yabo ga hukumar kiwon lafiya ta lardin Hunan na kasar Sin, wadda ta dauki nauyin tura tawagogin likitoci ga Zimbabwe cikin tsawon shekaru 38 da suka gabata. (Fa’iza Mustapha, Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Kudin Habasha Ya Yaba Da Kokarin Sin Kan Ci Gaban Kasa Mai Inganci

Next Post

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

Related

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

11 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

12 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

13 hours ago
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

14 hours ago
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

15 hours ago
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

17 hours ago
Next Post
Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

LABARAI MASU NASABA

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.