• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin jakadancin Sin dake Zimbabwe, ya gudanar da bikin cika shekaru 60 da fara tura tawagar jami’an lafiya na kasar Sin zuwa ketare, tare da maraba da tawaga ta 20 na jami’an lafiya da Sin ta tura kasar a ran 8 ga watan.

Haka kuma, bikin ya taya tawaga ta 19 ta jami’an lafiya ta kasar Sin, murnar kammala aikinsu na shekara 1 a kasar, cikin nasara.

Tun bayan da Sin ta tura tawaga ta farko ta jami’an lafiya zuwa kasar Algeria a 1963, kawo yanzu, ta tura jimilar jami’an lafiya 30,000, wadanda suka bada kulawar lafiya ga mutane miliyan 290 a kasashe da yankuna 76. Yanzu haka, tawagar jami’an lafiya na kasar Sin na aiki a birane 115 a kasashe 56 a fadin duniya.

Tun daga shekarar 1985 zuwa yanzu, kasar Sin ta tura tawagogin jami’an lafiya 20 zuwa kasar Zimbabwe. Kuma cikin shekarar da ta gabata, tawaga ta 19 ta yi aiki bisa hadin gwiwa da ma’aikatar lafiya ta kasar da sassa masu ruwa da tsaki, wajen samar da kiwon lafiya ga al’ummar Zimbabwe.

Da yake jawabi yayin bikin, mataimakin shugaban kasar Zimbabwe kuma ministan lafiya na kasar, Constantino Chiwenga, ya yaba da rawar da kasar da Sin da ma jami’an lafiyar suka taka wajen yaki da annobar COVID-19 a kasar. Yana mai cewa, kashin farko na alluran riga kafin cutar da ya shiga kasar a watan Fabrerun 2021, gudunmawa ce daga gwamnatin kasar Sin, lamarin da ya kaddamar da ganganmin riga kafi cikin nasara a kasar, inda zuwa yanzu ta yi wa kaso 60.8 na jama’arta riga kafi.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Sannan aka yi bikin mika aiki daga tawagar likitoci ta kasar Sin dake kasar Zimbabwe karo na 19 zuwa ta 20 a birnin Harare, inda mukaddashin jakadan Sin dake Zimbabwe Cheng Yan da mataimakin shugaban Zimbabwe kuma ministan kiwon lafiyar kasar Constantino Chiwenga suka halarci bikin.

A yayin bikin, a madadin gwamnatin Zimbabwe, minista Chiwenga ya ba da lambar yabo ga hukumar kiwon lafiya ta lardin Hunan na kasar Sin, wadda ta dauki nauyin tura tawagogin likitoci ga Zimbabwe cikin tsawon shekaru 38 da suka gabata. (Fa’iza Mustapha, Zainab Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Kudin Habasha Ya Yaba Da Kokarin Sin Kan Ci Gaban Kasa Mai Inganci

Next Post

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

Related

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

3 hours ago
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya
Daga Birnin Sin

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

4 hours ago
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

5 hours ago
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

6 hours ago
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

7 hours ago
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

8 hours ago
Next Post
Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.