ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Bikin Cika Shekaru 60 Da Sin Ta Fara Tura Tawagar Jami’an Lafiya Zuwa Ketare A Zimbabwe

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Ofishin jakadancin Sin dake Zimbabwe, ya gudanar da bikin cika shekaru 60 da fara tura tawagar jami’an lafiya na kasar Sin zuwa ketare, tare da maraba da tawaga ta 20 na jami’an lafiya da Sin ta tura kasar a ran 8 ga watan.

Haka kuma, bikin ya taya tawaga ta 19 ta jami’an lafiya ta kasar Sin, murnar kammala aikinsu na shekara 1 a kasar, cikin nasara.

Tun bayan da Sin ta tura tawaga ta farko ta jami’an lafiya zuwa kasar Algeria a 1963, kawo yanzu, ta tura jimilar jami’an lafiya 30,000, wadanda suka bada kulawar lafiya ga mutane miliyan 290 a kasashe da yankuna 76. Yanzu haka, tawagar jami’an lafiya na kasar Sin na aiki a birane 115 a kasashe 56 a fadin duniya.

ADVERTISEMENT

Tun daga shekarar 1985 zuwa yanzu, kasar Sin ta tura tawagogin jami’an lafiya 20 zuwa kasar Zimbabwe. Kuma cikin shekarar da ta gabata, tawaga ta 19 ta yi aiki bisa hadin gwiwa da ma’aikatar lafiya ta kasar da sassa masu ruwa da tsaki, wajen samar da kiwon lafiya ga al’ummar Zimbabwe.

Da yake jawabi yayin bikin, mataimakin shugaban kasar Zimbabwe kuma ministan lafiya na kasar, Constantino Chiwenga, ya yaba da rawar da kasar da Sin da ma jami’an lafiyar suka taka wajen yaki da annobar COVID-19 a kasar. Yana mai cewa, kashin farko na alluran riga kafin cutar da ya shiga kasar a watan Fabrerun 2021, gudunmawa ce daga gwamnatin kasar Sin, lamarin da ya kaddamar da ganganmin riga kafi cikin nasara a kasar, inda zuwa yanzu ta yi wa kaso 60.8 na jama’arta riga kafi.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

Sannan aka yi bikin mika aiki daga tawagar likitoci ta kasar Sin dake kasar Zimbabwe karo na 19 zuwa ta 20 a birnin Harare, inda mukaddashin jakadan Sin dake Zimbabwe Cheng Yan da mataimakin shugaban Zimbabwe kuma ministan kiwon lafiyar kasar Constantino Chiwenga suka halarci bikin.

A yayin bikin, a madadin gwamnatin Zimbabwe, minista Chiwenga ya ba da lambar yabo ga hukumar kiwon lafiya ta lardin Hunan na kasar Sin, wadda ta dauki nauyin tura tawagogin likitoci ga Zimbabwe cikin tsawon shekaru 38 da suka gabata. (Fa’iza Mustapha, Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

Ba A Son Raina Ummita Ta Rasu Ba –Dan China

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.