ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Zawarcin Sauran Mukaman Da Suka Rage A Majalisar Dattawa

by Abubakar Abba
2 years ago
Majalisar Dattawa

Biyo bayan kadddamar da majasilar dattatawa, inda Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga Kudu maso Kudu ya zamo shugaban majalisar, yayin da kuma mataimakinsa Sanata Barau Jibrin, ya fito daga Arewa ta Yamma, an fara gwagwarmar neman sauran mukamai da suka rage a majalisar ta 10.

Sauran manyan mukaman hudu da suka yi saura su ne, kujerar jagoran majalisar da ta mataimakinsa da ta mai tsawatarwa sai kuma ta mataimakin mai tsawatarwa wadanda aka tura su zuwa shiyoyyin Arewa ta Tsakiya, Arewa ta Yamma, Kudu maso Gabas da kuma Arewa maso Gabas
Baya ga Arewa ta Tsakiya da ke a cikin shiyoyin daukacin sauran shiyoyyin tuni sun samu wakilcin sun a manyan mukaman.

  • Sanata Barau Ya Zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa

Shugaba Bola Tinubu ya fito ne daga shiyayar Kudu maso Gabas, inda kuma da mataimakinsa Kashim Shettima, ya fito daga shiyyar Arewa maso Gabas.

ADVERTISEMENT

Rabar da manyan mukaman za su lura da na sauran shiyoyyin, sai dai, an bar shiyyar Arewa maso Tsakiya a baya saboda mukamin mataimakin mataimakin shugaban majalisar dattawa da na shugaban majalisar wakilia, sun tafi ne zuwa ga Arewa ta Yamma.

Amma wasu masu fashin baki sun yi jayayya kan cewa, kamata ya yi a ce kamata matsayin Sanata ya kasance jaogoran majalisar dattawa ne zai yi hakan don a yi adalaci, inda wasu kuma suka dage kai da fata cewa, dole ne a bi ka’ida.

LABARAI MASU NASABA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

A lokacin mulkin marigayi tsohon Shugaban Kasa, Umaru ‘Yar’adua, Aanata Teslim Folarin da ya fito daga Kudu maso Yamma shi ne jagoran majalisar ta dattawa, inda ya ci gaba da rike wannan mukamin har sai da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya cika wa’adin mulkin ‘Yar’adua.

Sanata Bictor Ndoma Egba da ya fito daga Kudu maso Kudu, ya zamo jagoran majalisar bayan an zabi Jonathan a matsayin shugaban kasa.

Bugu da kari, a 2019, Sanata Yahaya Abdullahi daga Jihar Kebbi ta Gabas, shi ne jagoran majalisar kafin ya sauya sheka zuwa PDP, inda kuma Sanata Ibrahim Gobir ya karbi jagorancin.

Ba wani tahrin a siyasar Nijeriya da ya tabbatar da ikirarin na su kan cewa, dole ne sai an mayar da mukamin na jagoran majalisar zuwa shiyyar shugaban kasa.

Har ila yau, idan aka yi dubi da ka’idar zamawo sanata, sanata Abdulfatai Buhari ne ya cancanta ganin cewa ya fito ne daga shiyyar Kudu maso Gabas, duba da ya kasance a majalisar wakilai a 2003, kafin a zabe shi sanata daga 2015 zuwa 2019 da kuma a 2023.

Sanata Solomon Adeola ne ke biye masa a baya, ganin cewa ya taba zama dan majalisar wakilai a 2011 kafin ya zama sanata a 2015, inda kuma aka sake zabarsa a 2015 da 2023.

A shiyyar Kudu maso Gabas kuwa, Sanata Orji Uzor Kalu da Osita Izunaso wadanda suka kasance manyan sanatoci biyu da suka fito daga Kudu maso Gabas, dukkan su sun taba zama a majalisar wakilai da kuma a majalisar datttawa har sau biyu.

Kalu ya taba zama a majalisar wakilai 1993, inda kuma Izunaso ya kasance a majalisar wakilai a 2007.

Lokacin da kawai Kalu ya kasance a majalisar wakilai, ya kai wata uku ne kawai kafin tsohowar mulkin soja ta marigayi Sani Abacha, ta yi juyin mulki.

Hakazalika, sanata Sani Musa da ya fito daga shiyyar Neja ta Gabas da kuma Saheed Umar, da ya fito daga Kwara ta Arewa, sun kasance su ne manyan sanatcin da ke kan gaba.

Daukacin su, sun kasance mayan sanatoci a majalisar dattawa har sau biyu daga 2019 zuwa 2023.

Manyan satocin da suka fito daga shiyyar Arewa ta Gabas, su ne Ahmad Lawan, wanda ya kasance shi ne tsohon shugaban majalisar ta 9 da ta kare sai kuma sanata Ali Ndume.

Sai dai, Lawan ba zai yarda ya zama jagoran majalisar ba, inda a yanzu ya rage ga Ndume, wanda ya ba da gagarumar gudunmawa wajen zamowar Bukola Saraki shugaban majalisar.

Ndume bai yi takara da sanata Danjuma Goje ba wajen neman babban mukamin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Sauya Sheka Zuwa APC Ba Zai Taimaki Tinuba Yin Tazarce Ba – Jam’iyyar ADC

December 19, 2025
‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Sun Yi Gargadi Kan Barazanar Dakile Dimokuradiyya Mai Jam’iyyu Da Dama

December 19, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Tambarin Dimokuradiyya

NNPP Ta Buƙaci INEC Ta Yi Watsi Da Tarukan Jam’iyyar Da Kwankwaso Zai Jagoranta

November 28, 2025
Next Post
Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.