• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Zawarcin Sauran Mukaman Da Suka Rage A Majalisar Dattawa

by Abubakar Abba
2 years ago
Majalisar Dattawa

Biyo bayan kadddamar da majasilar dattatawa, inda Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga Kudu maso Kudu ya zamo shugaban majalisar, yayin da kuma mataimakinsa Sanata Barau Jibrin, ya fito daga Arewa ta Yamma, an fara gwagwarmar neman sauran mukamai da suka rage a majalisar ta 10.

Sauran manyan mukaman hudu da suka yi saura su ne, kujerar jagoran majalisar da ta mataimakinsa da ta mai tsawatarwa sai kuma ta mataimakin mai tsawatarwa wadanda aka tura su zuwa shiyoyyin Arewa ta Tsakiya, Arewa ta Yamma, Kudu maso Gabas da kuma Arewa maso Gabas
Baya ga Arewa ta Tsakiya da ke a cikin shiyoyin daukacin sauran shiyoyyin tuni sun samu wakilcin sun a manyan mukaman.

  • Sanata Barau Ya Zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa

Shugaba Bola Tinubu ya fito ne daga shiyayar Kudu maso Gabas, inda kuma da mataimakinsa Kashim Shettima, ya fito daga shiyyar Arewa maso Gabas.

Rabar da manyan mukaman za su lura da na sauran shiyoyyin, sai dai, an bar shiyyar Arewa maso Tsakiya a baya saboda mukamin mataimakin mataimakin shugaban majalisar dattawa da na shugaban majalisar wakilia, sun tafi ne zuwa ga Arewa ta Yamma.

Amma wasu masu fashin baki sun yi jayayya kan cewa, kamata ya yi a ce kamata matsayin Sanata ya kasance jaogoran majalisar dattawa ne zai yi hakan don a yi adalaci, inda wasu kuma suka dage kai da fata cewa, dole ne a bi ka’ida.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

A lokacin mulkin marigayi tsohon Shugaban Kasa, Umaru ‘Yar’adua, Aanata Teslim Folarin da ya fito daga Kudu maso Yamma shi ne jagoran majalisar ta dattawa, inda ya ci gaba da rike wannan mukamin har sai da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya cika wa’adin mulkin ‘Yar’adua.

Sanata Bictor Ndoma Egba da ya fito daga Kudu maso Kudu, ya zamo jagoran majalisar bayan an zabi Jonathan a matsayin shugaban kasa.

Bugu da kari, a 2019, Sanata Yahaya Abdullahi daga Jihar Kebbi ta Gabas, shi ne jagoran majalisar kafin ya sauya sheka zuwa PDP, inda kuma Sanata Ibrahim Gobir ya karbi jagorancin.

Ba wani tahrin a siyasar Nijeriya da ya tabbatar da ikirarin na su kan cewa, dole ne sai an mayar da mukamin na jagoran majalisar zuwa shiyyar shugaban kasa.

Har ila yau, idan aka yi dubi da ka’idar zamawo sanata, sanata Abdulfatai Buhari ne ya cancanta ganin cewa ya fito ne daga shiyyar Kudu maso Gabas, duba da ya kasance a majalisar wakilai a 2003, kafin a zabe shi sanata daga 2015 zuwa 2019 da kuma a 2023.

Sanata Solomon Adeola ne ke biye masa a baya, ganin cewa ya taba zama dan majalisar wakilai a 2011 kafin ya zama sanata a 2015, inda kuma aka sake zabarsa a 2015 da 2023.

A shiyyar Kudu maso Gabas kuwa, Sanata Orji Uzor Kalu da Osita Izunaso wadanda suka kasance manyan sanatoci biyu da suka fito daga Kudu maso Gabas, dukkan su sun taba zama a majalisar wakilai da kuma a majalisar datttawa har sau biyu.

Kalu ya taba zama a majalisar wakilai 1993, inda kuma Izunaso ya kasance a majalisar wakilai a 2007.

Lokacin da kawai Kalu ya kasance a majalisar wakilai, ya kai wata uku ne kawai kafin tsohowar mulkin soja ta marigayi Sani Abacha, ta yi juyin mulki.

Hakazalika, sanata Sani Musa da ya fito daga shiyyar Neja ta Gabas da kuma Saheed Umar, da ya fito daga Kwara ta Arewa, sun kasance su ne manyan sanatcin da ke kan gaba.

Daukacin su, sun kasance mayan sanatoci a majalisar dattawa har sau biyu daga 2019 zuwa 2023.

Manyan satocin da suka fito daga shiyyar Arewa ta Gabas, su ne Ahmad Lawan, wanda ya kasance shi ne tsohon shugaban majalisar ta 9 da ta kare sai kuma sanata Ali Ndume.

Sai dai, Lawan ba zai yarda ya zama jagoran majalisar ba, inda a yanzu ya rage ga Ndume, wanda ya ba da gagarumar gudunmawa wajen zamowar Bukola Saraki shugaban majalisar.

Ndume bai yi takara da sanata Danjuma Goje ba wajen neman babban mukamin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.