ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Zawarcin Sauran Mukaman Da Suka Rage A Majalisar Dattawa

by Abubakar Abba
3 years ago
Majalisar Dattawa

Biyo bayan kadddamar da majasilar dattatawa, inda Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga Kudu maso Kudu ya zamo shugaban majalisar, yayin da kuma mataimakinsa Sanata Barau Jibrin, ya fito daga Arewa ta Yamma, an fara gwagwarmar neman sauran mukamai da suka rage a majalisar ta 10.

Sauran manyan mukaman hudu da suka yi saura su ne, kujerar jagoran majalisar da ta mataimakinsa da ta mai tsawatarwa sai kuma ta mataimakin mai tsawatarwa wadanda aka tura su zuwa shiyoyyin Arewa ta Tsakiya, Arewa ta Yamma, Kudu maso Gabas da kuma Arewa maso Gabas
Baya ga Arewa ta Tsakiya da ke a cikin shiyoyin daukacin sauran shiyoyyin tuni sun samu wakilcin sun a manyan mukaman.

  • Sanata Barau Ya Zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa

Shugaba Bola Tinubu ya fito ne daga shiyayar Kudu maso Gabas, inda kuma da mataimakinsa Kashim Shettima, ya fito daga shiyyar Arewa maso Gabas.

ADVERTISEMENT

Rabar da manyan mukaman za su lura da na sauran shiyoyyin, sai dai, an bar shiyyar Arewa maso Tsakiya a baya saboda mukamin mataimakin mataimakin shugaban majalisar dattawa da na shugaban majalisar wakilia, sun tafi ne zuwa ga Arewa ta Yamma.

Amma wasu masu fashin baki sun yi jayayya kan cewa, kamata ya yi a ce kamata matsayin Sanata ya kasance jaogoran majalisar dattawa ne zai yi hakan don a yi adalaci, inda wasu kuma suka dage kai da fata cewa, dole ne a bi ka’ida.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A lokacin mulkin marigayi tsohon Shugaban Kasa, Umaru ‘Yar’adua, Aanata Teslim Folarin da ya fito daga Kudu maso Yamma shi ne jagoran majalisar ta dattawa, inda ya ci gaba da rike wannan mukamin har sai da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya cika wa’adin mulkin ‘Yar’adua.

Sanata Bictor Ndoma Egba da ya fito daga Kudu maso Kudu, ya zamo jagoran majalisar bayan an zabi Jonathan a matsayin shugaban kasa.

Bugu da kari, a 2019, Sanata Yahaya Abdullahi daga Jihar Kebbi ta Gabas, shi ne jagoran majalisar kafin ya sauya sheka zuwa PDP, inda kuma Sanata Ibrahim Gobir ya karbi jagorancin.

Ba wani tahrin a siyasar Nijeriya da ya tabbatar da ikirarin na su kan cewa, dole ne sai an mayar da mukamin na jagoran majalisar zuwa shiyyar shugaban kasa.

Har ila yau, idan aka yi dubi da ka’idar zamawo sanata, sanata Abdulfatai Buhari ne ya cancanta ganin cewa ya fito ne daga shiyyar Kudu maso Gabas, duba da ya kasance a majalisar wakilai a 2003, kafin a zabe shi sanata daga 2015 zuwa 2019 da kuma a 2023.

Sanata Solomon Adeola ne ke biye masa a baya, ganin cewa ya taba zama dan majalisar wakilai a 2011 kafin ya zama sanata a 2015, inda kuma aka sake zabarsa a 2015 da 2023.

A shiyyar Kudu maso Gabas kuwa, Sanata Orji Uzor Kalu da Osita Izunaso wadanda suka kasance manyan sanatoci biyu da suka fito daga Kudu maso Gabas, dukkan su sun taba zama a majalisar wakilai da kuma a majalisar datttawa har sau biyu.

Kalu ya taba zama a majalisar wakilai 1993, inda kuma Izunaso ya kasance a majalisar wakilai a 2007.

Lokacin da kawai Kalu ya kasance a majalisar wakilai, ya kai wata uku ne kawai kafin tsohowar mulkin soja ta marigayi Sani Abacha, ta yi juyin mulki.

Hakazalika, sanata Sani Musa da ya fito daga shiyyar Neja ta Gabas da kuma Saheed Umar, da ya fito daga Kwara ta Arewa, sun kasance su ne manyan sanatcin da ke kan gaba.

Daukacin su, sun kasance mayan sanatoci a majalisar dattawa har sau biyu daga 2019 zuwa 2023.

Manyan satocin da suka fito daga shiyyar Arewa ta Gabas, su ne Ahmad Lawan, wanda ya kasance shi ne tsohon shugaban majalisar ta 9 da ta kare sai kuma sanata Ali Ndume.

Sai dai, Lawan ba zai yarda ya zama jagoran majalisar ba, inda a yanzu ya rage ga Ndume, wanda ya ba da gagarumar gudunmawa wajen zamowar Bukola Saraki shugaban majalisar.

Ndume bai yi takara da sanata Danjuma Goje ba wajen neman babban mukamin ba.

Majalisar Dattawa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

Bikin Sallar Layya: Gwamnatin Katsina Ta Ayyana Hutun Mako Guda Ga Makarantu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.