• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana zargin gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda da yin rufa-rufa a kan kudaden da aka kashe wajen sayen masara domin raba wa al’umma.

Rahotanni sun ce gwamna Dikko Umar Radda ne ya bada umarnin sayen masara buhu 36,100 domin raba wa a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina da niyyar rage radadin rayuwa da ake fama da shi.

  • Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa
  • Dan Bindiga Ya Harbe Mutum Da Raunata Wasu Da Dama A Amurka

To sai dai batun da ya dabaibaye wannan shiri na bada tallafi shi ne, yadda gwamnati tun daga gwamna zuwa Kwamishinoni da shuwagabannin Kananan hukumomi suka yi gum wajen kin bayyana ko nawa aka ware domin yin wannan hidima.

Yanzu haka yatsan zargi na nuna cewa akwai wani abu da ake boyewa a kan wannan shiri na raban kayan abinci wanda wasu mutane suka ce tiya daya ta masara suka samu wasu kuma suke ce sun samu gwangwanin shinkafa uku duk da sunan tallafi.

Shugaban karamar hukumar Kaita kuma shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi, injiniya Bello Yandaki ya bayyana cewa wannan tallafi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar Katsina da kuma kananan hukumomi inda kowane bangare zai bada kashi 50.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

Wannan yunkuri da gwamnati ta yi da yawa jama’a sun kalle shi ta fuskar taimako da rage radadin mawuyacin halin da aka shiga wannan gwamnati ga Bola Ahmad Tinubu.

Dangane da batun ko nawa aka ware domin sayo wadanda kayayyaki ya bayyana cewa shi dai na karamar hukumar sa kawai ya sani bai san na saura ba.

Ganin yadda shugaban kungiyar shuwagabannin Kananan hukumomi ya ja daga cewa baya da ikon bayyana ko nawa aka kashe yasa yatsan zargi ke nuna gwamnatin Dikko Radda da yin rufa-rufa da kudaden ƙananan hukumomi wanda ya ce zai sakar masu mara su yi fitsari idan ya zama gwamna.

Wani abu da ke ba jama’a mamaki a kan wannan lamari shi ne yadda manyan jami’an gwamnatin jihar Katsina suka yi gum da bakinsu wajan bayyanawa duniya makudan Kudaden da aka kashe wajen bada wannan tallafi da wasu suka samu tiyar masara daya wasu kuma suka kare da gwangwanin shinkafa uku.

Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu na jihar Katsina Farfesa Badamasi Charanci na daga cikin jami’an gwamnati da ya kamata su maganta amma yaki yarda ya hadu da ‘yan jarida domin tattaunawa a kan wannan batu.

Shima kwamishinan ma’aikatar yaɗa labarai Hon. Bala Zango ya shafawa idanunsa toka inda ya bayyana cewa Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu ne ke da alhakin yin wannan bayani ba shi ba.

Wani dalili da ke saya ana yi wa gwamnatin jihar Katsina kallon hadarin kaji game da kin bayyana ko nawa ta kashe wajan sayen masara da aka raba a Kananan hukumomi shi ne, yadda gwamnati ta bayyana karbar Naira biliyan 2 sannan ta bada umarnin a sayi shinkafa buhu 40,000 da kudin baki daya.

Yanzu haka jama’a da dama na kallon wannan abu tamkar wata rufa-rufa ce da kudaden jama’a da gwamnatin Dikko Raɗɗa ta yi rantsuwa cewa za ta kula da su kuma ta yi amfani da su yadda ya kamata.

To sai dai ko me ya sa suke tsoron bayyanawa duniya cewa ga adadin kudaden da aka kashe domin sayen masara buhu dubu 36,100 wanda aka raba shi ga kowace mazaba buhu 100.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaKatsinaTallafiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Next Post

CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

3 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

4 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

5 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

7 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

9 hours ago
Next Post
CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.