• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana zargin gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda da yin rufa-rufa a kan kudaden da aka kashe wajen sayen masara domin raba wa al’umma.

Rahotanni sun ce gwamna Dikko Umar Radda ne ya bada umarnin sayen masara buhu 36,100 domin raba wa a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina da niyyar rage radadin rayuwa da ake fama da shi.

  • Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa
  • Dan Bindiga Ya Harbe Mutum Da Raunata Wasu Da Dama A Amurka

To sai dai batun da ya dabaibaye wannan shiri na bada tallafi shi ne, yadda gwamnati tun daga gwamna zuwa Kwamishinoni da shuwagabannin Kananan hukumomi suka yi gum wajen kin bayyana ko nawa aka ware domin yin wannan hidima.

Yanzu haka yatsan zargi na nuna cewa akwai wani abu da ake boyewa a kan wannan shiri na raban kayan abinci wanda wasu mutane suka ce tiya daya ta masara suka samu wasu kuma suke ce sun samu gwangwanin shinkafa uku duk da sunan tallafi.

Shugaban karamar hukumar Kaita kuma shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi, injiniya Bello Yandaki ya bayyana cewa wannan tallafi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar Katsina da kuma kananan hukumomi inda kowane bangare zai bada kashi 50.

Labarai Masu Nasaba

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

Wannan yunkuri da gwamnati ta yi da yawa jama’a sun kalle shi ta fuskar taimako da rage radadin mawuyacin halin da aka shiga wannan gwamnati ga Bola Ahmad Tinubu.

Dangane da batun ko nawa aka ware domin sayo wadanda kayayyaki ya bayyana cewa shi dai na karamar hukumar sa kawai ya sani bai san na saura ba.

Ganin yadda shugaban kungiyar shuwagabannin Kananan hukumomi ya ja daga cewa baya da ikon bayyana ko nawa aka kashe yasa yatsan zargi ke nuna gwamnatin Dikko Radda da yin rufa-rufa da kudaden ƙananan hukumomi wanda ya ce zai sakar masu mara su yi fitsari idan ya zama gwamna.

Wani abu da ke ba jama’a mamaki a kan wannan lamari shi ne yadda manyan jami’an gwamnatin jihar Katsina suka yi gum da bakinsu wajan bayyanawa duniya makudan Kudaden da aka kashe wajen bada wannan tallafi da wasu suka samu tiyar masara daya wasu kuma suka kare da gwangwanin shinkafa uku.

Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu na jihar Katsina Farfesa Badamasi Charanci na daga cikin jami’an gwamnati da ya kamata su maganta amma yaki yarda ya hadu da ‘yan jarida domin tattaunawa a kan wannan batu.

Shima kwamishinan ma’aikatar yaɗa labarai Hon. Bala Zango ya shafawa idanunsa toka inda ya bayyana cewa Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu ne ke da alhakin yin wannan bayani ba shi ba.

Wani dalili da ke saya ana yi wa gwamnatin jihar Katsina kallon hadarin kaji game da kin bayyana ko nawa ta kashe wajan sayen masara da aka raba a Kananan hukumomi shi ne, yadda gwamnati ta bayyana karbar Naira biliyan 2 sannan ta bada umarnin a sayi shinkafa buhu 40,000 da kudin baki daya.

Yanzu haka jama’a da dama na kallon wannan abu tamkar wata rufa-rufa ce da kudaden jama’a da gwamnatin Dikko Raɗɗa ta yi rantsuwa cewa za ta kula da su kuma ta yi amfani da su yadda ya kamata.

To sai dai ko me ya sa suke tsoron bayyanawa duniya cewa ga adadin kudaden da aka kashe domin sayen masara buhu dubu 36,100 wanda aka raba shi ga kowace mazaba buhu 100.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dikko RaddaKatsinaTallafiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Yi Nuni Ga Ikon BRICS Na Juya Akalar Harkokin Duniya Zuwa Hanya Mai Bullewa

Next Post

CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

Related

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

1 minute ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

46 minutes ago
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa
Labarai

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

12 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

13 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

18 hours ago
Next Post
CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

LABARAI MASU NASABA

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

August 2, 2025
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.