• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Katsina

Ana zargin gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda da yin rufa-rufa a kan kudaden da aka kashe wajen sayen masara domin raba wa al’umma.

Rahotanni sun ce gwamna Dikko Umar Radda ne ya bada umarnin sayen masara buhu 36,100 domin raba wa a kananan hukumomi 34 na jihar Katsina da niyyar rage radadin rayuwa da ake fama da shi.

  • Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa
  • Dan Bindiga Ya Harbe Mutum Da Raunata Wasu Da Dama A Amurka

To sai dai batun da ya dabaibaye wannan shiri na bada tallafi shi ne, yadda gwamnati tun daga gwamna zuwa Kwamishinoni da shuwagabannin Kananan hukumomi suka yi gum wajen kin bayyana ko nawa aka ware domin yin wannan hidima.

Yanzu haka yatsan zargi na nuna cewa akwai wani abu da ake boyewa a kan wannan shiri na raban kayan abinci wanda wasu mutane suka ce tiya daya ta masara suka samu wasu kuma suke ce sun samu gwangwanin shinkafa uku duk da sunan tallafi.

Shugaban karamar hukumar Kaita kuma shugaban kungiyar shugabannin kananan hukumomi, injiniya Bello Yandaki ya bayyana cewa wannan tallafi hadin gwiwa ne tsakanin gwamnatin jihar Katsina da kuma kananan hukumomi inda kowane bangare zai bada kashi 50.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Wannan yunkuri da gwamnati ta yi da yawa jama’a sun kalle shi ta fuskar taimako da rage radadin mawuyacin halin da aka shiga wannan gwamnati ga Bola Ahmad Tinubu.

Dangane da batun ko nawa aka ware domin sayo wadanda kayayyaki ya bayyana cewa shi dai na karamar hukumar sa kawai ya sani bai san na saura ba.

Ganin yadda shugaban kungiyar shuwagabannin Kananan hukumomi ya ja daga cewa baya da ikon bayyana ko nawa aka kashe yasa yatsan zargi ke nuna gwamnatin Dikko Radda da yin rufa-rufa da kudaden ƙananan hukumomi wanda ya ce zai sakar masu mara su yi fitsari idan ya zama gwamna.

Wani abu da ke ba jama’a mamaki a kan wannan lamari shi ne yadda manyan jami’an gwamnatin jihar Katsina suka yi gum da bakinsu wajan bayyanawa duniya makudan Kudaden da aka kashe wajen bada wannan tallafi da wasu suka samu tiyar masara daya wasu kuma suka kare da gwangwanin shinkafa uku.

Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu na jihar Katsina Farfesa Badamasi Charanci na daga cikin jami’an gwamnati da ya kamata su maganta amma yaki yarda ya hadu da ‘yan jarida domin tattaunawa a kan wannan batu.

Shima kwamishinan ma’aikatar yaɗa labarai Hon. Bala Zango ya shafawa idanunsa toka inda ya bayyana cewa Kwamishinan Kananan hukumomi da masarautu ne ke da alhakin yin wannan bayani ba shi ba.

Wani dalili da ke saya ana yi wa gwamnatin jihar Katsina kallon hadarin kaji game da kin bayyana ko nawa ta kashe wajan sayen masara da aka raba a Kananan hukumomi shi ne, yadda gwamnati ta bayyana karbar Naira biliyan 2 sannan ta bada umarnin a sayi shinkafa buhu 40,000 da kudin baki daya.

Yanzu haka jama’a da dama na kallon wannan abu tamkar wata rufa-rufa ce da kudaden jama’a da gwamnatin Dikko Raɗɗa ta yi rantsuwa cewa za ta kula da su kuma ta yi amfani da su yadda ya kamata.

To sai dai ko me ya sa suke tsoron bayyanawa duniya cewa ga adadin kudaden da aka kashe domin sayen masara buhu dubu 36,100 wanda aka raba shi ga kowace mazaba buhu 100.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.