• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An zargi wani jami’in hukumar shige da fice ta kasa mai suna Lamba da harbe wani mai zanga-zanga Jacob Bamgbola har lahira a yankin Idigbo da ke Karamar Hukumar Yewa ta Arewa a Jihar Ogun.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa Bamgbola yana kan hanyarsa ta kai wata ‘yar kanwarsa a wata unguwa akan babur, sai wasu jami’an shige da fice da ke aiki a shingen bincike a kan babbar hanyar suka tare shi a kan titin Ijowun na babban titin Idiroko inda suka bukaci ya basu Naira 200 kafin su bar shi ya wuce.

  • Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa
  • Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Da NATO Ta Yi Mata

Wakilinmu ya gano cewa Bamgbola ya ki amincewa da bukatar jami’an, inda ya fada musu cewa ta yaya bai yi wani laifi ba kuma za a karbi kudi har Naira 200 a hannunsa.

Lamarin dai ya haifar da cece-kuce, a can gefe kuma wasu daga cikin jami’an suka ci gaba tambayar sauran masu ababan hawa kudi, sai Benjamin ya yi amfani da wannan damar ya shammace su kawai ya ja babur dinsa zai tafiyarsa.

Lokacin da ya isa wurin da zai je sai a kjiye ‘yar uwar tasa, bayan da Bamgbola ya ajiye ‘yar uwarsa, sai ya ci gaba da ba wa wasu matasan wurin labarin yadda suka yi da da jami’an shige da ficen.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Wata majiya a unguwar ta shaida wa wakilinmu cewa, matasan, wadanda suma sun fuskanci irin wannan matsalar ta karbar kudin da jami’an shige-da-fice suke yi a kan hanyar, sun tara wasu matasa zuwa gidan wani basarake a yankin, Moses Faleye, domin nuna rashin amincewarsu da hakan.

Majiyar ta ce a yayin zanga-zangar, jami’an shige-da-ficen sun kutsa kai cikin harabar, kuma a lokacin da suke kokarin tarwatsa masu zanga-zangar, a wannan yanayi ne aka yi zargin sun harbe Bamgbola har lahira.

Ya ce, “Bamgbola ya je daukar ‘yar ‘yar uwarsa, kuma a kan hanyarsa ta dawowa ya hadu da jami’an shige-da-fice a hanya. Wadannan jami’an koyaushe suna can a shingen binciken. Sun dakatar da shi suna so su karbar masa Naira 200 amma ya ki.

“Ya ce musu shi dan kauyen Otun ne kuma me zai sa ya biya su komai. Bayan ya tafi ne ya kai kara ga wasu matasa inda matasan suka hada kansu zuwa gidan Baale domin yin rajistar kokensu kan ayyukan jami’an.

“Amma cikin ‘yan mintoci kadan jami’an hukumar shige-da-fice sun zo da mota a lokacin da Baale ke kokarin shawo kan lamarin, sai suka fara harbe-harbe, ana cikin haka sai daya daga cikinsu mai suna Lamba ya harbe Bamgbola. Matasan sun garzaya da Bamgbola asibiti inda a wannan lokacin lilkitoci suka tabbatar da ya rasu.”

Shugaban kungiyar ‘yan banga a garin, Adesina Alabi, yayin da ya koka kan faruwar lamarin, ya ce jami’an tsaro na sha’awar karbar kudade daga masu amfani da hanyar a kan hanyar.

“Kawai za ka ga ’yan sanda, jami’an Kwastam, jami’an shige-da-fice, da sauran su kawai babu abin da suke yi sai katbar kudi a shingayen hanya daga hannun masu ababen hawa. Yana kara yawa,” inji shi.

Da aka tuntubi Falaye, ya ce lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar Bamgbola abin takaici ne, inda ya ce kamata ya yi a sasanta lamarin.

Ya ce, “A gaban gidana lamarin ya faru. Matasan garin sun zo ne domin nuna rashin jin dadinsu kan ayyukan jami’an shige da fice a yankinmu.

“A lokacin da nake kokarin sasanta su, wasu jami’an shige-da-fice sun zo, da suka ga matasan sai suka fara harbin iska. Ana cikin haka ne harsashin ya samu mutum daya ya mutu.

“Bayan faruwar lamarin, an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Igbokofi kuma ‘yan sandan sun zo da kyamarori kuma sun karbi bayanai daga gare mu.”

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar, SP Omolola Odutola, ta shaida wa wakilinmu cewa ba ta da masaniya a kan lamarin, amma ta yi alkawarin za ta nemi wakilinmu da zarar lamarin ya zo gare ta.

Har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoton ba ta ce komai ba.

Da aka tuntubi mai magana da yawun NIS a Jihar, Olajide Oshifeso, ya ce, “an riga an fara bincike kan lamarin kuma idan an kamala za a bayyana wa jama’a cikakkun bayanai.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KisaNISZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Next Post

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 month ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 month ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 month ago
Next Post
Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

LABARAI MASU NASABA

Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.