ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NIS

An zargi wani jami’in hukumar shige da fice ta kasa mai suna Lamba da harbe wani mai zanga-zanga Jacob Bamgbola har lahira a yankin Idigbo da ke Karamar Hukumar Yewa ta Arewa a Jihar Ogun.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa Bamgbola yana kan hanyarsa ta kai wata ‘yar kanwarsa a wata unguwa akan babur, sai wasu jami’an shige da fice da ke aiki a shingen bincike a kan babbar hanyar suka tare shi a kan titin Ijowun na babban titin Idiroko inda suka bukaci ya basu Naira 200 kafin su bar shi ya wuce.

  • Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa
  • Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Da NATO Ta Yi Mata

Wakilinmu ya gano cewa Bamgbola ya ki amincewa da bukatar jami’an, inda ya fada musu cewa ta yaya bai yi wani laifi ba kuma za a karbi kudi har Naira 200 a hannunsa.

ADVERTISEMENT

Lamarin dai ya haifar da cece-kuce, a can gefe kuma wasu daga cikin jami’an suka ci gaba tambayar sauran masu ababan hawa kudi, sai Benjamin ya yi amfani da wannan damar ya shammace su kawai ya ja babur dinsa zai tafiyarsa.

Lokacin da ya isa wurin da zai je sai a kjiye ‘yar uwar tasa, bayan da Bamgbola ya ajiye ‘yar uwarsa, sai ya ci gaba da ba wa wasu matasan wurin labarin yadda suka yi da da jami’an shige da ficen.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Wata majiya a unguwar ta shaida wa wakilinmu cewa, matasan, wadanda suma sun fuskanci irin wannan matsalar ta karbar kudin da jami’an shige-da-fice suke yi a kan hanyar, sun tara wasu matasa zuwa gidan wani basarake a yankin, Moses Faleye, domin nuna rashin amincewarsu da hakan.

Majiyar ta ce a yayin zanga-zangar, jami’an shige-da-ficen sun kutsa kai cikin harabar, kuma a lokacin da suke kokarin tarwatsa masu zanga-zangar, a wannan yanayi ne aka yi zargin sun harbe Bamgbola har lahira.

Ya ce, “Bamgbola ya je daukar ‘yar ‘yar uwarsa, kuma a kan hanyarsa ta dawowa ya hadu da jami’an shige-da-fice a hanya. Wadannan jami’an koyaushe suna can a shingen binciken. Sun dakatar da shi suna so su karbar masa Naira 200 amma ya ki.

“Ya ce musu shi dan kauyen Otun ne kuma me zai sa ya biya su komai. Bayan ya tafi ne ya kai kara ga wasu matasa inda matasan suka hada kansu zuwa gidan Baale domin yin rajistar kokensu kan ayyukan jami’an.

“Amma cikin ‘yan mintoci kadan jami’an hukumar shige-da-fice sun zo da mota a lokacin da Baale ke kokarin shawo kan lamarin, sai suka fara harbe-harbe, ana cikin haka sai daya daga cikinsu mai suna Lamba ya harbe Bamgbola. Matasan sun garzaya da Bamgbola asibiti inda a wannan lokacin lilkitoci suka tabbatar da ya rasu.”

Shugaban kungiyar ‘yan banga a garin, Adesina Alabi, yayin da ya koka kan faruwar lamarin, ya ce jami’an tsaro na sha’awar karbar kudade daga masu amfani da hanyar a kan hanyar.

“Kawai za ka ga ’yan sanda, jami’an Kwastam, jami’an shige-da-fice, da sauran su kawai babu abin da suke yi sai katbar kudi a shingayen hanya daga hannun masu ababen hawa. Yana kara yawa,” inji shi.

Da aka tuntubi Falaye, ya ce lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar Bamgbola abin takaici ne, inda ya ce kamata ya yi a sasanta lamarin.

Ya ce, “A gaban gidana lamarin ya faru. Matasan garin sun zo ne domin nuna rashin jin dadinsu kan ayyukan jami’an shige da fice a yankinmu.

“A lokacin da nake kokarin sasanta su, wasu jami’an shige-da-fice sun zo, da suka ga matasan sai suka fara harbin iska. Ana cikin haka ne harsashin ya samu mutum daya ya mutu.

“Bayan faruwar lamarin, an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Igbokofi kuma ‘yan sandan sun zo da kyamarori kuma sun karbi bayanai daga gare mu.”

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar, SP Omolola Odutola, ta shaida wa wakilinmu cewa ba ta da masaniya a kan lamarin, amma ta yi alkawarin za ta nemi wakilinmu da zarar lamarin ya zo gare ta.

Har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoton ba ta ce komai ba.

Da aka tuntubi mai magana da yawun NIS a Jihar, Olajide Oshifeso, ya ce, “an riga an fara bincike kan lamarin kuma idan an kamala za a bayyana wa jama’a cikakkun bayanai.”

NIS
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.