ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NIS

An zargi wani jami’in hukumar shige da fice ta kasa mai suna Lamba da harbe wani mai zanga-zanga Jacob Bamgbola har lahira a yankin Idigbo da ke Karamar Hukumar Yewa ta Arewa a Jihar Ogun.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa Bamgbola yana kan hanyarsa ta kai wata ‘yar kanwarsa a wata unguwa akan babur, sai wasu jami’an shige da fice da ke aiki a shingen bincike a kan babbar hanyar suka tare shi a kan titin Ijowun na babban titin Idiroko inda suka bukaci ya basu Naira 200 kafin su bar shi ya wuce.

  • Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa
  • Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Da NATO Ta Yi Mata

Wakilinmu ya gano cewa Bamgbola ya ki amincewa da bukatar jami’an, inda ya fada musu cewa ta yaya bai yi wani laifi ba kuma za a karbi kudi har Naira 200 a hannunsa.

ADVERTISEMENT

Lamarin dai ya haifar da cece-kuce, a can gefe kuma wasu daga cikin jami’an suka ci gaba tambayar sauran masu ababan hawa kudi, sai Benjamin ya yi amfani da wannan damar ya shammace su kawai ya ja babur dinsa zai tafiyarsa.

Lokacin da ya isa wurin da zai je sai a kjiye ‘yar uwar tasa, bayan da Bamgbola ya ajiye ‘yar uwarsa, sai ya ci gaba da ba wa wasu matasan wurin labarin yadda suka yi da da jami’an shige da ficen.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Wata majiya a unguwar ta shaida wa wakilinmu cewa, matasan, wadanda suma sun fuskanci irin wannan matsalar ta karbar kudin da jami’an shige-da-fice suke yi a kan hanyar, sun tara wasu matasa zuwa gidan wani basarake a yankin, Moses Faleye, domin nuna rashin amincewarsu da hakan.

Majiyar ta ce a yayin zanga-zangar, jami’an shige-da-ficen sun kutsa kai cikin harabar, kuma a lokacin da suke kokarin tarwatsa masu zanga-zangar, a wannan yanayi ne aka yi zargin sun harbe Bamgbola har lahira.

Ya ce, “Bamgbola ya je daukar ‘yar ‘yar uwarsa, kuma a kan hanyarsa ta dawowa ya hadu da jami’an shige-da-fice a hanya. Wadannan jami’an koyaushe suna can a shingen binciken. Sun dakatar da shi suna so su karbar masa Naira 200 amma ya ki.

“Ya ce musu shi dan kauyen Otun ne kuma me zai sa ya biya su komai. Bayan ya tafi ne ya kai kara ga wasu matasa inda matasan suka hada kansu zuwa gidan Baale domin yin rajistar kokensu kan ayyukan jami’an.

“Amma cikin ‘yan mintoci kadan jami’an hukumar shige-da-fice sun zo da mota a lokacin da Baale ke kokarin shawo kan lamarin, sai suka fara harbe-harbe, ana cikin haka sai daya daga cikinsu mai suna Lamba ya harbe Bamgbola. Matasan sun garzaya da Bamgbola asibiti inda a wannan lokacin lilkitoci suka tabbatar da ya rasu.”

Shugaban kungiyar ‘yan banga a garin, Adesina Alabi, yayin da ya koka kan faruwar lamarin, ya ce jami’an tsaro na sha’awar karbar kudade daga masu amfani da hanyar a kan hanyar.

“Kawai za ka ga ’yan sanda, jami’an Kwastam, jami’an shige-da-fice, da sauran su kawai babu abin da suke yi sai katbar kudi a shingayen hanya daga hannun masu ababen hawa. Yana kara yawa,” inji shi.

Da aka tuntubi Falaye, ya ce lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar Bamgbola abin takaici ne, inda ya ce kamata ya yi a sasanta lamarin.

Ya ce, “A gaban gidana lamarin ya faru. Matasan garin sun zo ne domin nuna rashin jin dadinsu kan ayyukan jami’an shige da fice a yankinmu.

“A lokacin da nake kokarin sasanta su, wasu jami’an shige-da-fice sun zo, da suka ga matasan sai suka fara harbin iska. Ana cikin haka ne harsashin ya samu mutum daya ya mutu.

“Bayan faruwar lamarin, an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Igbokofi kuma ‘yan sandan sun zo da kyamarori kuma sun karbi bayanai daga gare mu.”

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar, SP Omolola Odutola, ta shaida wa wakilinmu cewa ba ta da masaniya a kan lamarin, amma ta yi alkawarin za ta nemi wakilinmu da zarar lamarin ya zo gare ta.

Har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoton ba ta ce komai ba.

Da aka tuntubi mai magana da yawun NIS a Jihar, Olajide Oshifeso, ya ce, “an riga an fara bincike kan lamarin kuma idan an kamala za a bayyana wa jama’a cikakkun bayanai.”

NIS
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.