ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Jami’in NIS Da Bindige Mai Zanga-zanga A Ogun

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NIS

An zargi wani jami’in hukumar shige da fice ta kasa mai suna Lamba da harbe wani mai zanga-zanga Jacob Bamgbola har lahira a yankin Idigbo da ke Karamar Hukumar Yewa ta Arewa a Jihar Ogun.

PUNCH Metro ta ruwaito cewa Bamgbola yana kan hanyarsa ta kai wata ‘yar kanwarsa a wata unguwa akan babur, sai wasu jami’an shige da fice da ke aiki a shingen bincike a kan babbar hanyar suka tare shi a kan titin Ijowun na babban titin Idiroko inda suka bukaci ya basu Naira 200 kafin su bar shi ya wuce.

  • Xi Ya Nanata Bukatar Samun Ci Gaba Mai Inganci A Fannin Tsaron Intanet Da Aikin Sadarwa
  • Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Da NATO Ta Yi Mata

Wakilinmu ya gano cewa Bamgbola ya ki amincewa da bukatar jami’an, inda ya fada musu cewa ta yaya bai yi wani laifi ba kuma za a karbi kudi har Naira 200 a hannunsa.

ADVERTISEMENT

Lamarin dai ya haifar da cece-kuce, a can gefe kuma wasu daga cikin jami’an suka ci gaba tambayar sauran masu ababan hawa kudi, sai Benjamin ya yi amfani da wannan damar ya shammace su kawai ya ja babur dinsa zai tafiyarsa.

Lokacin da ya isa wurin da zai je sai a kjiye ‘yar uwar tasa, bayan da Bamgbola ya ajiye ‘yar uwarsa, sai ya ci gaba da ba wa wasu matasan wurin labarin yadda suka yi da da jami’an shige da ficen.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Wata majiya a unguwar ta shaida wa wakilinmu cewa, matasan, wadanda suma sun fuskanci irin wannan matsalar ta karbar kudin da jami’an shige-da-fice suke yi a kan hanyar, sun tara wasu matasa zuwa gidan wani basarake a yankin, Moses Faleye, domin nuna rashin amincewarsu da hakan.

Majiyar ta ce a yayin zanga-zangar, jami’an shige-da-ficen sun kutsa kai cikin harabar, kuma a lokacin da suke kokarin tarwatsa masu zanga-zangar, a wannan yanayi ne aka yi zargin sun harbe Bamgbola har lahira.

Ya ce, “Bamgbola ya je daukar ‘yar ‘yar uwarsa, kuma a kan hanyarsa ta dawowa ya hadu da jami’an shige-da-fice a hanya. Wadannan jami’an koyaushe suna can a shingen binciken. Sun dakatar da shi suna so su karbar masa Naira 200 amma ya ki.

“Ya ce musu shi dan kauyen Otun ne kuma me zai sa ya biya su komai. Bayan ya tafi ne ya kai kara ga wasu matasa inda matasan suka hada kansu zuwa gidan Baale domin yin rajistar kokensu kan ayyukan jami’an.

“Amma cikin ‘yan mintoci kadan jami’an hukumar shige-da-fice sun zo da mota a lokacin da Baale ke kokarin shawo kan lamarin, sai suka fara harbe-harbe, ana cikin haka sai daya daga cikinsu mai suna Lamba ya harbe Bamgbola. Matasan sun garzaya da Bamgbola asibiti inda a wannan lokacin lilkitoci suka tabbatar da ya rasu.”

Shugaban kungiyar ‘yan banga a garin, Adesina Alabi, yayin da ya koka kan faruwar lamarin, ya ce jami’an tsaro na sha’awar karbar kudade daga masu amfani da hanyar a kan hanyar.

“Kawai za ka ga ’yan sanda, jami’an Kwastam, jami’an shige-da-fice, da sauran su kawai babu abin da suke yi sai katbar kudi a shingayen hanya daga hannun masu ababen hawa. Yana kara yawa,” inji shi.

Da aka tuntubi Falaye, ya ce lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar Bamgbola abin takaici ne, inda ya ce kamata ya yi a sasanta lamarin.

Ya ce, “A gaban gidana lamarin ya faru. Matasan garin sun zo ne domin nuna rashin jin dadinsu kan ayyukan jami’an shige da fice a yankinmu.

“A lokacin da nake kokarin sasanta su, wasu jami’an shige-da-fice sun zo, da suka ga matasan sai suka fara harbin iska. Ana cikin haka ne harsashin ya samu mutum daya ya mutu.

“Bayan faruwar lamarin, an kai rahoton lamarin a ofishin ‘yansanda na Igbokofi kuma ‘yan sandan sun zo da kyamarori kuma sun karbi bayanai daga gare mu.”

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sandan jihar, SP Omolola Odutola, ta shaida wa wakilinmu cewa ba ta da masaniya a kan lamarin, amma ta yi alkawarin za ta nemi wakilinmu da zarar lamarin ya zo gare ta.

Har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoton ba ta ce komai ba.

Da aka tuntubi mai magana da yawun NIS a Jihar, Olajide Oshifeso, ya ce, “an riga an fara bincike kan lamarin kuma idan an kamala za a bayyana wa jama’a cikakkun bayanai.”

NIS
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

Abin Da Ya Sa Na Mika Dala 80,000 Da Na Tsinta A Saudiya —Hajiya Aishatu Nahuce

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.