ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
Amurka

Jiya Laraba ne ministar kasuwancin kasar Amurka Gina Raimondo ta kammala ziyarar aikinta na kwanaki 4 a kasar Sin, wadda ita ce babbar jami’ar Amurka ta hudu da ta ziyarci kasar Sin tun daga watan Yunin bana. 

Dangane da ziyararta, akasarin ra’ayoyin jama’a sun mai da hankali kan yadda Sin da Amurka suka sanar da kafa sabuwar hanyar tuntubar juna, matakin da suke ganin cewa, zai taimaka wajen rage rashin fahimtar juna a tsakanin kasashen 2. Kana Madam Raimondo ta bayyana a fili cewa, Amurka ba ta neman raba-gari da Sin, tare da fatan kamfanonin Amurka za su zuba jari a kasar Sin.

  • CMG Da Kamfanin Watsa Labaran Afirka Ta Kudu Za Su Yi Hadin Gwiwar Shirya Shirin Talabijin Na “Documentary”

Masana sun bayyana wa wakilin CMG cewa, sabuwar hanyar tuntubar juna tsakanin Sin da Afirka, za ta taimakawa kasashen 2 wajen inganta tuntubar juna da mu’amalar juna, amma yadda sabuwar hanyar tuntubar junar za ta yi aiki yadda ya kamata, zai danganta da abin da Amurka za ta yi.

ADVERTISEMENT

Ana fatan Amurka za ta aiwatar da kudurin kin raba-gari da Sin, ba kawai domin ci gaban huldar cinikayya a tsakanin kasashen 2 ba, har ma domin biyan bukatun sassan masana’antu da kasuwanci na kasashen 2, lamarin da zai amfana wa bunkasar tattalin arzikinsu da ma na duniya baki daya. Abin da ya zama wajibi Amurka ta yi yanzu shi ne, hanzarta soke harajin da take kara dora wa kasar Sin, dakatar da takunkumin da take sanyawa kayayyakin kasar Sin, da soke takunkuminta kan kamfanonin kasar Sin, a kokarin ganin kamfanonin kasashen 2 sun kara yin ciniki, zuba jari da hada kai.

Huldar tattalin arziki da cinikayya, tushe ne na huldar da ke tsakanin kasashen Sin da Amurka. Ana fatan sabuwar hanyar tuntubar junar za ta kasance a matsayin sabon mafari. Wato fatan Amurka za ta nuna sahihanci wajen daidaita matsaloli, za ta dauki matakai kamar yadda kasar Sin ta yi, za ta kara azama kan kyautata hulda a tsakaninta da Sin, da farfadowar tattalin arzikin duniya. Bayan ziyarar Raimondo, kasashen duniya na zura ido kan matakin da Amurka za ta dauka. (Tasallah Yuan)

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

An Kashe 'Yan Ta'adda 39, An kama 159 A Borno Da Yobe

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.