ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Ta’adda 39, An kama 159 A Borno Da Yobe

by Abubakar Abba
3 years ago
Ta'adda

Sojin rundunar Operation Hadin Kai, sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwanton bauna, wanda hakan ya ba su nasarar kashe 39 tare da kama 159 daga cikinsu. 

Kazalika, sojin sun kuma ceto mutane 109 da masu garkuwa suka sace a waje daban-daban.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin
  • Dan Daba Ya Yi Wa Dan Jarida Dukan Tsiya A Cikin Gidan Gwamnatin Adamawa

Daraktan yada labarai na rundunar tsaro Majo Janar Edward Buba, ya shaida wa manema labarai hakan a yau Alhamis shalkwatar rundunar da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ce, rundunar sojin kasa, ta lashi tokobin ci gaba da dakile masu son yi wa kasar nan zagon kasa na samun ‘yanci.

Ya ci gaba da cewa, jirgin sojin sama ya yi luguden wuta a wani sansanin ‘yan bindiga a dajin Sububu da ke a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina, inda suka tarwatsa sansanin nasu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

Bugu da kari, ya ce sojin sun kuma yi wa wasu manyan ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP kwanton bauna, inda suka kama su, a Gwoza da Tarmuwa da ke a Borno da kuma Yobe.

A cewarsa, hakan ya kuma tilasta wasu daga cikin ‘yan ta’addar mika wuya a Gwoza da ke a jihar Borno, inda a wannan nasara, sojin suka kashe wasu ‘yan ta’addar suma kuma ceto mutanen da suka sace tare da kwato makamai da albarusai.

Bugu da kari, sojin a wani aikin da suka yi, sun hallaka ‘yan ta’adda 11, sun cafke 45 sun kuma ceto mutane 34, tare da kuma kwato makamai da albarusai.

Ya ce, daga cikin makaman sun hada da, bindigun AK-47 shida, bindiga daya kirar HK21, bindiga daya kirar GPMG, bindiga kirar gida guda daya, kunshin albarusai guda 11 da sauransu.

Ya ce, sojin rundunar Operation Safe Haven da ke aiki a Arewa ta Tsakiya, sun kashe ‘yan bindiga biyu sun kuma ceto mutane uku da aka sace tare da kuma kama ‘yan bindiga 15.

Kazalika, ya ce sojin rundunar Operation Delta Safe a mako biyun da suka gabata, sun kama wasu da ake zargin barayin mai ne a yankin Neja Delta da kuma mutane 34 da sarrafa haramtacciyar matatar mai, wadda sojin suka lalata.

Bugu da kari Buba ya sanar da sojin sun kuma dakile yunkurin masu satar mai, tare da kwace kudi Naira miliyan 765.8 a wajensu da kama makamai guda 55 da albarusai guda 96.

Ta'adda
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

September 16, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

September 16, 2026
Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose
Manyan Labarai

Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

September 16, 2026
Next Post
Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

Gwamnan Kano Ya Naɗa Hafsat Kutama Mukaddashiyar Shugabar Hukumar PCACC 

September 16, 2026
Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku

Rokar Gravity-1 Na Kasar Sin Ya Harba Sabbin Taurarin Dan’adam Daga Teku

September 16, 2026
TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

TCN Ta Samar Da Hanyar Samun Wutar Lantarki A Kebbi Ta Wucin Gadi

September 16, 2026
APC Ta Tsawaita Rijistar Mambobinta, Ta Ɗage Ranar Babban Taronta Na Ƙasa

APC Ta Nemi A Gudanar Da Bincike Kan Farmakin Da A Kai Ofisoshinta A Kaduna

September 16, 2026
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Ban Taɓa Yi Wa Tinubu Alƙawarin Zan Koma APC Ba – Wike

September 16, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Sama Da 1,100 Cikin Shekara Ɗaya – Kwamanda

September 16, 2026
Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

Tinubu Zai Kayar Da Atiku Da Obi Ko Da Sun Haɗa Kai – Fayose

September 16, 2026
Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

Jarumin Nollywood Olu Jacobs Ya Rasu Yana Da Shekaru 84

September 16, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

September 16, 2026
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Gwamnati Ba Ta Da Hurumin Ɗaukar Nauyin Yi Wa Mutane Aure – Dino Melaye

September 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.