ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Ta’adda 39, An kama 159 A Borno Da Yobe

by Abubakar Abba
3 years ago
Ta'adda

Sojin rundunar Operation Hadin Kai, sun yi wa wasu ‘yan bindiga kwanton bauna, wanda hakan ya ba su nasarar kashe 39 tare da kama 159 daga cikinsu. 

Kazalika, sojin sun kuma ceto mutane 109 da masu garkuwa suka sace a waje daban-daban.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin
  • Dan Daba Ya Yi Wa Dan Jarida Dukan Tsiya A Cikin Gidan Gwamnatin Adamawa

Daraktan yada labarai na rundunar tsaro Majo Janar Edward Buba, ya shaida wa manema labarai hakan a yau Alhamis shalkwatar rundunar da ke Abuja.

ADVERTISEMENT

Ya ce, rundunar sojin kasa, ta lashi tokobin ci gaba da dakile masu son yi wa kasar nan zagon kasa na samun ‘yanci.

Ya ci gaba da cewa, jirgin sojin sama ya yi luguden wuta a wani sansanin ‘yan bindiga a dajin Sububu da ke a karamar hukumar Kankara ta Jihar Katsina, inda suka tarwatsa sansanin nasu.

LABARAI MASU NASABA

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

Bugu da kari, ya ce sojin sun kuma yi wa wasu manyan ‘yan ta’addar Boko Haram da na ISWAP kwanton bauna, inda suka kama su, a Gwoza da Tarmuwa da ke a Borno da kuma Yobe.

A cewarsa, hakan ya kuma tilasta wasu daga cikin ‘yan ta’addar mika wuya a Gwoza da ke a jihar Borno, inda a wannan nasara, sojin suka kashe wasu ‘yan ta’addar suma kuma ceto mutanen da suka sace tare da kwato makamai da albarusai.

Bugu da kari, sojin a wani aikin da suka yi, sun hallaka ‘yan ta’adda 11, sun cafke 45 sun kuma ceto mutane 34, tare da kuma kwato makamai da albarusai.

Ya ce, daga cikin makaman sun hada da, bindigun AK-47 shida, bindiga daya kirar HK21, bindiga daya kirar GPMG, bindiga kirar gida guda daya, kunshin albarusai guda 11 da sauransu.

Ya ce, sojin rundunar Operation Safe Haven da ke aiki a Arewa ta Tsakiya, sun kashe ‘yan bindiga biyu sun kuma ceto mutane uku da aka sace tare da kuma kama ‘yan bindiga 15.

Kazalika, ya ce sojin rundunar Operation Delta Safe a mako biyun da suka gabata, sun kama wasu da ake zargin barayin mai ne a yankin Neja Delta da kuma mutane 34 da sarrafa haramtacciyar matatar mai, wadda sojin suka lalata.

Bugu da kari Buba ya sanar da sojin sun kuma dakile yunkurin masu satar mai, tare da kwace kudi Naira miliyan 765.8 a wajensu da kama makamai guda 55 da albarusai guda 96.

Ta'adda
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci
Manyan Labarai

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Next Post
Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

Bukatar Samar Da Kariya Ta Musamman Ga Makarantunmu

LABARAI MASU NASABA

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026
Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

Kasar Sin Za Ta Habaka Bude Fannonin Hada-Hadar Kudi Ga Duniya

June 17, 2026
Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

Sin Na Gaggauta Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Kasa Da Kasa

June 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.