• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Carlo Ancelotti ya amince da karbar ragamar horar da tawagar ‘yan wasan kasar Brazil a shekara ta 2024, in ji shugaban hukumar kwallon kafa ta kasar, Ednaldo Rodrigues.

Brazil, wadda ta lashe gasar cin kofin duniya sau biyar ta yi amannar cewa dan kasar Italiyan shi ne ya fi dacewa da ya kai Brazil Copa America da za a yi a watan Yunin 2024.

  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Rodrigues ya ce mai koyarwa Fernando Diniz zai ci gaba da lura da kungiyar ta Brazil da ake kira Selacao tare da ci gaba da aikinsa na horar da Flumine har zuwa lokacin da Ancelotti zai karbi aiki wato idan kwantiraginsa ya kare da Real Madrid.

“Shi ne zai mika wa Ancelotti ragamar Brazil kuma salon wasansa ya yi kusa da na kocin da zai karbi aikin kai kungiyar gasar cin kofin Copa America, wato mista Ancelotti” in ji Rodrigues.

Ya ci gaba da cewa ba za su kira shi kocin rikon kwarya ba ga tawagarsu ta kasa,

Labarai Masu Nasaba

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Brazil dai ta kasance ba ta da mai koyarwa tun bayan kammala gasar kofin duniya da aka kammala a bara, lokacin da Tite ya ajiye aiki bayan cire kasar da Croatia ta yi a wasan kusa da daf da na karshe.

Kocin da ke jan ragamar tawagar ‘yan kasa da shekara 20 ne ke lura da Brazil a wasanni sa da zumunta da take yi a kwanakin nan kuma Ancelotti mai shekara 64 ya koma Real Madrid ne a shekarar 2021 bayan ya bar Eberton, kuma tun bayan komarwarsa ya ci Champions da La Liga da Copa del Rey da sauransu.

Da kofin zakarun Turai da ya lashe a 2022 a wasan karshe a hannun Liberpool, Ancelotti ya lashe kofin nahiyar Turai na hudu kenan a matsayinsa na koci, na biyu a Real Madrid bayan biyu da ya lashe a AC Milan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AncelottiBrazilKociReal Madrid
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Dikko Ya Amince Da Bude Asusun Bai-daya A Jihar Katsina

Next Post

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Related

Lookman
Wasanni

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

2 hours ago
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG
Wasanni

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

2 days ago
Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya
Wasanni

Isak Na Dab Da Zama Ɗan Wasa Mafi Tsada A Tarihin Firimiya

3 days ago
Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana
Wasanni

Yadda Kungiyoyin Firimiyar Ingila Suka Shirya Wa Kakar Bana

4 days ago
‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana
Wasanni

‘Yan Wasan Afirka Da Ake Ganin Za Su Yi Abin Kirki A Kakar Bana

4 days ago
Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United
Wasanni

Rasmus Højlund Ya Sauya Sheƙa Zuwa Napoli A Matsayin Aro Daga Manchester United

4 days ago
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

September 3, 2025
Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

September 3, 2025
Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi 

September 3, 2025
Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

Kasar Sin Ta Shirya Bikin Gala Na Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yakin Turjiyar Jama’ar Kasar Da Yaki Da Mulkin Danniya A Duniya

September 3, 2025
Lookman

Kofin Duniya: Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

September 3, 2025
Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

Firaministan Senegal: Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa 

September 3, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

September 3, 2025
Shettima

Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima

September 3, 2025
Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

Shekaru 80 Na Nasara: Kasar Sin Ta Nuna Gado Mai Kyau Na Yaki Da Zalunci

September 3, 2025
Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.