• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ancelotti Zai Zama Kociyan Tawagar Brazil A 2024

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Brazil

Mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid Carlo Ancelotti ya amince da karbar ragamar horar da tawagar ‘yan wasan kasar Brazil a shekara ta 2024, in ji shugaban hukumar kwallon kafa ta kasar, Ednaldo Rodrigues.

Brazil, wadda ta lashe gasar cin kofin duniya sau biyar ta yi amannar cewa dan kasar Italiyan shi ne ya fi dacewa da ya kai Brazil Copa America da za a yi a watan Yunin 2024.

  • Kiwon Lafiya: Yadda Dabi’un Ko-in-kula Ke Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • Ribadu Zai Shugabanci Taron LEADERSHIP Da NDLEA Kan Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Rodrigues ya ce mai koyarwa Fernando Diniz zai ci gaba da lura da kungiyar ta Brazil da ake kira Selacao tare da ci gaba da aikinsa na horar da Flumine har zuwa lokacin da Ancelotti zai karbi aiki wato idan kwantiraginsa ya kare da Real Madrid.

“Shi ne zai mika wa Ancelotti ragamar Brazil kuma salon wasansa ya yi kusa da na kocin da zai karbi aikin kai kungiyar gasar cin kofin Copa America, wato mista Ancelotti” in ji Rodrigues.

Ya ci gaba da cewa ba za su kira shi kocin rikon kwarya ba ga tawagarsu ta kasa,

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Brazil dai ta kasance ba ta da mai koyarwa tun bayan kammala gasar kofin duniya da aka kammala a bara, lokacin da Tite ya ajiye aiki bayan cire kasar da Croatia ta yi a wasan kusa da daf da na karshe.

Kocin da ke jan ragamar tawagar ‘yan kasa da shekara 20 ne ke lura da Brazil a wasanni sa da zumunta da take yi a kwanakin nan kuma Ancelotti mai shekara 64 ya koma Real Madrid ne a shekarar 2021 bayan ya bar Eberton, kuma tun bayan komarwarsa ya ci Champions da La Liga da Copa del Rey da sauransu.

Da kofin zakarun Turai da ya lashe a 2022 a wasan karshe a hannun Liberpool, Ancelotti ya lashe kofin nahiyar Turai na hudu kenan a matsayinsa na koci, na biyu a Real Madrid bayan biyu da ya lashe a AC Milan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
Wasanni

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta
Labarai

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
Wasanni

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Next Post
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

LABARAI MASU NASABA

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.