• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase

by Bashir Bello, Abuja
2 years ago
apc

Mataimakin kakakin Majalisar wakilai ta tarayyar Nijeriya a zauren Majalisa karo na tara, Honarabul Ahmed Idris Wase ya yi ikirarin cewa Jam’iyyarsu ta APC za ta yi nasara da rinjaye mai girma a zaben shugabancin majalisar ta 10 da za a rantsar.

Dan Majalisar mai wakiltar mazabar Wase ta Jihar Filato, kuma wanda ya kasance daya daga cikin yan takarar Kujerar shugabancin Majalisar wakilai a zauren Majalisar, ya bayyana hakan ne a wani zantawar sa da manema labarai a garin Abuja.

  • An Kashe Fitacciyar Mawaƙiyar Nan Ta Sudan Shaden Gardoodd

 

Idris Wase, ya kara da cewa a bisa shirye-shiryen da su ke, sun samu gabatar da taro na niyyar su ta neman shugabancin Majalisar Kasa na kujerar kakakin Majalisar wakilan tarayyar kasar kuma suna ganin sun kai gabar da ya kamata su fada wa mutane ‘yan Jam’iyyar su, masoya tare da magoya baya cewa lokaci ya kai.

“Duk da cewa akwai ‘yan Jam’iyyar adawa da su ma suke ganin za su iya hada kai su nema, ina mai tabbatar da cewa Jam’iyyar APC ce za ta yi nasara da rinjaye ta samu shugabancin Majalisar.”

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

“A game da Batun Shiyya-Shiyya wacce uwar Jam’iyya ta ke kokarin shirin yi, mun san wani abu ne wanda ya saba wa ka’idar kundin tsarin mulkin Nijeriya domin sashe na 14 cikin 3, ya bayyana cewa ya kamata a raba mukamai bisa ga shiyyoyi ko Jihohi idan zai kai amma idan ba zai kai ba shi ne za a yi bisa ga shiyya-shiyya.

“Don haka wannan shi ne tsarin da muke da shi na Jagorancin shugabancin Kasa na shugaban kasa, shugaban Majalisar Dattijai da Majalisar wakilai Hakazalika da na mataimakan su wanda su ne guda shida domin kawo tsarin zaman lafiya da ingancin zamantakewa amma kamar an manta da wannan Dokar.”

“Ni dan Jam’iyya ne kuma na yarda da tsarin dokokin Jam’iyya kuma na tabbata idan Jam’iyya ta yi za mu yi kuma dama can yan Majalisa ne ke da hakkin yin zaɓe kamar yadda kundin tsarin mulkin ya tanada kuma duk abin da ake yi ana tuntuba ne domin a ga yaya za a yi a kai ga nasara ta yadda ba za a samu hayaniya ba domin zaɓe ba ya gabata sai an Shiga cikin Majalisa.” In ji Shi.

Acewar Idris Wase, kamar yadda ya zo ya bayyana cewa yana neman shugabancin Majalisar, ai akwai wadanda su ma suka zo suna nema daga Jam’iyyarsu ta APC wanda suke da kyakkyawar alaka da tunani don haka ya kamata su hada kai su fitar da wanda suke ganin zai iya yin aikin daga cikin su shi yasa suke tattaunawa a kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Next Post
Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Kasashen Sin Da Na Yankin Tsakiyar Asiya Ya Cimma Manyan Sakamako

Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Kasashen Sin Da Na Yankin Tsakiyar Asiya Ya Cimma Manyan Sakamako

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.