ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ce Za Ta Yi Nasarar Samar Da Shugabanci A Majalisa – Hon. Wase

by Bashir Bello, Abuja
3 years ago
apc

Mataimakin kakakin Majalisar wakilai ta tarayyar Nijeriya a zauren Majalisa karo na tara, Honarabul Ahmed Idris Wase ya yi ikirarin cewa Jam’iyyarsu ta APC za ta yi nasara da rinjaye mai girma a zaben shugabancin majalisar ta 10 da za a rantsar.

Dan Majalisar mai wakiltar mazabar Wase ta Jihar Filato, kuma wanda ya kasance daya daga cikin yan takarar Kujerar shugabancin Majalisar wakilai a zauren Majalisar, ya bayyana hakan ne a wani zantawar sa da manema labarai a garin Abuja.

  • An Kashe Fitacciyar Mawaƙiyar Nan Ta Sudan Shaden Gardoodd

 

ADVERTISEMENT

Idris Wase, ya kara da cewa a bisa shirye-shiryen da su ke, sun samu gabatar da taro na niyyar su ta neman shugabancin Majalisar Kasa na kujerar kakakin Majalisar wakilan tarayyar kasar kuma suna ganin sun kai gabar da ya kamata su fada wa mutane ‘yan Jam’iyyar su, masoya tare da magoya baya cewa lokaci ya kai.

“Duk da cewa akwai ‘yan Jam’iyyar adawa da su ma suke ganin za su iya hada kai su nema, ina mai tabbatar da cewa Jam’iyyar APC ce za ta yi nasara da rinjaye ta samu shugabancin Majalisar.”

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“A game da Batun Shiyya-Shiyya wacce uwar Jam’iyya ta ke kokarin shirin yi, mun san wani abu ne wanda ya saba wa ka’idar kundin tsarin mulkin Nijeriya domin sashe na 14 cikin 3, ya bayyana cewa ya kamata a raba mukamai bisa ga shiyyoyi ko Jihohi idan zai kai amma idan ba zai kai ba shi ne za a yi bisa ga shiyya-shiyya.

“Don haka wannan shi ne tsarin da muke da shi na Jagorancin shugabancin Kasa na shugaban kasa, shugaban Majalisar Dattijai da Majalisar wakilai Hakazalika da na mataimakan su wanda su ne guda shida domin kawo tsarin zaman lafiya da ingancin zamantakewa amma kamar an manta da wannan Dokar.”

“Ni dan Jam’iyya ne kuma na yarda da tsarin dokokin Jam’iyya kuma na tabbata idan Jam’iyya ta yi za mu yi kuma dama can yan Majalisa ne ke da hakkin yin zaɓe kamar yadda kundin tsarin mulkin ya tanada kuma duk abin da ake yi ana tuntuba ne domin a ga yaya za a yi a kai ga nasara ta yadda ba za a samu hayaniya ba domin zaɓe ba ya gabata sai an Shiga cikin Majalisa.” In ji Shi.

Acewar Idris Wase, kamar yadda ya zo ya bayyana cewa yana neman shugabancin Majalisar, ai akwai wadanda su ma suka zo suna nema daga Jam’iyyarsu ta APC wanda suke da kyakkyawar alaka da tunani don haka ya kamata su hada kai su fitar da wanda suke ganin zai iya yin aikin daga cikin su shi yasa suke tattaunawa a kai.

apc
Bashir Bello, Abuja
+ postsBio
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Sanata Kaka Lawan Ya Gabatar Da Kudirin Tattara Dokokin Nijeriya Na Tsawon Shekara 19
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Kudirin Gaggauta Aikin Makarantar Kwastam A Bauchi
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Ba Za Mu Lamunci Dauki-Dora A Shugabancin Majalisa Ba —Kawu Sumaila
  • Bashir Bello, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/bashir-bello-abuja/
    Shugabancin Majalisa: Na Fi Kowa Cancanta, Ni Kadai Na Kawo Kudiri 78, Guda 21 Shugaban Kasa Ya Sa Wa Hannu – Hon Abbas Tajudeen

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Kasashen Sin Da Na Yankin Tsakiyar Asiya Ya Cimma Manyan Sakamako

Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Kasashen Sin Da Na Yankin Tsakiyar Asiya Ya Cimma Manyan Sakamako

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.