• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS

by Bello Hamza and Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Asalin Abin Da Ya Faru Tsakanin Abba Gida-gida Da Uwargidan Shugaban DSS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

A makon jiya ne aka samu wata takaddama a tsakanin dan takarar gwamnan Jihar Kano a karkashin jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida-gida da Uwargidar shugaban Hukumar DSS Aisha Yusuf Bichi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a yayin da magoya bayan mutanen biyu suka tayar da jijiyar wuya a tsakanin su har ta kai ga furuce-furuce a kafafen sadarwa na zamani, Wakilanmu sun bi diddigi don gano asalin abin da ya faru da kuma yadda abin ya nemi ya tunbatsa har ya kusan daukar sabon salo.

Matar babban daraktan tsaro na farin Kaya na kasa (DSS) ta sa an tsare dan takarar kujerar Gwamnan Kano na Jam’iyyar NNPP na Kano Injiniya Abba Kabir Yusif Wanda a kafi sani da (Abba Gida-gida) tare da bada umarnin lakadawa hadiminsa duka a filin sauka da tashin jirgen sama a Malam Aminu Kano.

  • Turkashi: Aisha Bichi Ta Ce Jami’an Tsaron Farin Kaya Su Kamo Mata Abba Gida-Gida

Kamar yadda rahotanni suka nuna mai dakin babban Darakta hukumar jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Aisha Yusuf Bichi, ta bada umarnin a tsare dan takarar Gwamnan na jam’iyyar NNPP a Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ta hana shi hawa jirgi da ga Kano zuwa Abuja.
Dambarwar ta faru ne a kofar shiga bangaren matafiya masu ido da Kwalli (alfarma) na filin sauka da tashin jirgen sama na Malam Aminu Kano, yayin da ayarin motocin Abba Kabir Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-gida, su ka haifar da cinkoso a lokacin da ita uwargidan Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ke Kan hanyarta ta shiga filin Jirgin.
Lamarin da ya haifar wa da ayarin motocin da ke tare a taron Aisha Bichi tsaiko, yayin da ta ke shiga bangaren masu ido da kwallin domin tashi zuwa Abuja.
Wannan cunkoso da motocin wancan dan takara ya haifar ne ya fusata Aisha Bichi, inda dogarawanta su ka rika duka kan mai uwa da wabi da ababen hawa saboda raina Hajiya da suke zargin tawagar wancan dan takara ya yi.
Shaidun gani da ido sun ce da kurar ta lafa, sai shi Injiniya Abba Abba Kabir Yusif (Abba Gida-gida) ya je don ya yi mata korafin abinda dogaranta su ka yi, a matsayin ta na kawar mai dakinsa, inda ta nuna matukar bacin ranta, har ta ke cewa ba za ta bari ya zama Gwamna a Kano ba.
Daga nan dai, in ji majiyoyi, sai ga karin jami’an tsaron farin kaya sun zo, inda su ka tsare Abba Gida-gida har sai da Aisha Bichi ta shiga jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin ma sun ce kafin ta tashi zuwa Abuja, a lokacin da ta ke ta fada, Aisha Bichi ta hango wani hadimin Abba Gida-gida, Garba Kilo yana daukar ta a waya, inda ta sa dogaran ta su “Harbe shi kuma ba abin da za a yi.” a cewar majiyar data nemi a sakaya sunanta.
Uwar Gidan babban Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta ci gaba da fada, ta kuma rantse cewa Abba Gida-gida ba zai shiga jirgi daya da ita ba. Haka dai aka ci gaba da tsare Abba har sai da jirgin ya tashi da matar Daraktan,” in ji majiyar.
Lamarin ya faru ranar Lahadin data gabata, amma kuma wata majiya da bamu tabbatar da sahihancinta ta rawaito cewa, Uwargidan Daraktan Hukumar tsaron farin kayan ta je har gida inda ta baiwa shi Abba Kabir Yusif hakuri bayan jan kunenta da maigidanta ya yi tare da umartarta take ta bashi hakuri.
Alhaji Abba Gwale shima ya yi tsokaci Kan wannan sabata juyetan da ke kara haska wani lamari da ke bukatar yi wa kallon tsanaki, inda ya bayyana cewa, Duk Nijeriya mutane 15 doka ta sahalewa yin amfani da jiniya (Amsa Kuwwa). A ciki babu shugaban jami’an tsaro na farin kaya ballantana matar sa, kuma hukuncin yin amfani da jiniya ga wanda doka bata amince masa ba.
A wani bangare kuma, Shugaban hukumar DSS Yusuf Magaji Bichi, ya bayyana cewa, ya bayyana cewa, ya gano wani shiri na musamman da wasu suka nyi don bata masa suna dana iyalansa, wannan kuma yana faruwa ne saboda mastayarsa ba kan wasu kururin gwamnati da kuma yadda yake gabatar da aikinsa ba tare da tsoro ba.
Ya ce wadannan mutane sun shirya amfani da kungiyoyi masu zaman kansu wajen shirya zanga-zanga da taruka inda za su yi kokarin bata masa suna dana iyalansa.
Yusuf Bichi ya na magana ne a takardar sanarwa da mai magana da yawujn hukumar DSS, Peter Afunanya ya sanya wa hannun aka kuma raba wa manema labarai a Abuja. Ya kuma tabbatar da faruwar takaddama a tsakanin matar Yusuf Bichi da dan takarar gwamnan Jihar kano na jami’iyyar NNPP a filin jigin saman a Malam Aminu Kano inda jami’an DSS da ke rakiyar Aisha Bich suka dakatar da Abba Gida-gida shiga jirgin saman, suna mayar da martani ne bayan da motocin da ke cikin tawagar Abba Gida-gida suka tare hanya abin da ya jawo wa Aisha Bichi jinkiri ita da jama’ar ta.
Sanarwa ta kara da cewa, “Hukumar DSS ba za ta zura ido tana kallon wasu gungun jama’a suna furucin raini ga shugaban da ma’aiakatan hukumar ba saboda wata mastalar da suke fuskanta, kuna kuma kira ga al’umma da su yi watsi da duk wata farfaganda na batanci da za a yi na bata sunan shugaban hukumar.
“Muna kuma kara jaddada goyon bayanmu ga shugaban kasa za kuma mu ci gaba da fuskantar duk wata barazana da ke nemi kawo cikas ga zaman lafiyar kasar nan musamman zaben da ke tafe a cikin wannan shekarar.” In ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Next Post

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

1 day ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

5 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

6 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

1 week ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Next Post
Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

Boko Haram Damfara Ce Da Aka Shirya Don Tarwatsa Nijeriya Kawai -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.