• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Da Daliban Jami’o’i Suka Tafka Sakamakon Yajin Aikin ASUU

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
in Rahotonni
0
ASUU
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daliban jami’o’in Nijeriya an tilasta masu rasa karatu har na tsawon shekara hudu wannan sakamakon yawan yajin aikin da Kungiyar Malaman jami’o’i ta Kasa (ASUU), suke tafiya tun lokacin da aka dawo mulkin farar hula gadan- gadan a shekarar 1999.

Binciken da Jaridar LEADERSHIP ta yi ya nuna yajin aikin da kungiyar ASUU take yi a halin yanzu shi ne na goma 16 tun da Nijeriya ta koma mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999.

  • Ma’aikatan Jiragen Sama Za Su Rufe Filayen Jirage Don Nuna Goyan Bayansu Ga ASUU A Yajin Aikin Da Suke

An rufe jami’o’in gwamnati fiye da shekaru 4 cikin shekara 23, wanda lokaci ne da ya kamata a ce an kammala karatun digiri, yayin da ake samun yajin aikin da yake kai makonni, wani yajin aikin kuma yake kai watanni.

Yawan yajin aiki mai dadewa da kungiyar ASUU take yi abu ne wanda yake damun dalibai, iyayensu, da kuma masu ruwa da tsaki kan al’amarin da ya shafi ilmi.

Shekaru da yawa jami’o’in Nijeriya sun sha fuskantar matsaloli na rashin ba su kudaden da suka kamata a ba su don gudanar da ayyukansu. Ga dai kuma rashin isassun kayan da suka dace a ce suna amfani da su, wannan kuma abin an dade ana fuskantar hakan tun daga gwamnatocin da suka shude, abin har yanzu an rasa yadda za a maganin al’amarin.

Labarai Masu Nasaba

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

ASUU kungiya ce ta ma’aikata wadda aka kafa ta shekarar 1978 domin ta kare muradan malaman jami’o’in gwamnatin tarayya da na Jihohi, saboda kuwa babbar manufarsu ita ce kare mutuncinsu da kuma mu’amala tsakanin malaman jami’o’i da wadanda suka daukesu aiki, al’amarin da kullum yana kasancewa zaman doya da manja.

A karskashin mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, dalibai da ke karatu a jami’o’in Nijeriya sun rasa zagon karatu na watanni 13.

Hakan ya faru ne sanadiyar yajin aikin da Kungiyar ASUU ke tsunduma. Shi ya sa kwararru a bangaren ilimi suke cewa wadanda suka kammala karatunsu a jami’o’in Nijeriya, ba a daukarsu da wata daraja kamar wadanda suka yi karatu a kasashen waje.

Karkashin mulkin Shugaban Kasa Buhari, kungiyar ta fara shiga yajin aiki ne a ranar 17 ga Agustan 2017, bayan da gwamnati ta ki cika masu alkawarin da suka sa hannu a yarjejeniyar da suka yi.

Daga cikin fiye da naira tiriliyan daya da ASUU ta bukaci a ba ta, naira biliyan 200 ne kadai aka ba ta wannan kuma shi ne ya sa kungiyar ta shiga yajin aikin gargadi a watan Nuwamba 2016, domin a biya masu bukatunsu. An koma aiki ne a watan Satumba 2017.

Yajin aikin kungiyar ASUU na biyu an fara shi ne ranar 4 ga Nuwamban 2018, wanda ya kai zuwa 7 ga Fabarairun 2019, an yi kwana 95, wannan kuma ya faru ne sakamakon wasu al’amuran da ba a gama da su ba tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar na yarjejeniya da aka sa hannu ga bangarorin biyu a shekarar 2013.

A yanzu haka dai, sanadiyar yajin aikin ASUU, Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) za ta fara zanga- zangar goyon bayan a ranar 26 ga watan Yulin 2022.

Kungiyar ta ce babbar matsalar ita ce, rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya ta sa hannu da maganar aiwatar da su a shekarar 2019, domin kuwa dukkan jami’an gwamnati da na kungiyar sun amince da hakan.

Wadannan kuma sun hada da wani tsarin biyan su albashi da alawus da jin dadinsu da samun ‘yancin kan da ya shafi harkokin koyarwa da dai sauran su.

Bugu da kari binciken LEADERSHIP ya gano cewa saboda yawan tafiya yajin aiki da kungiyar take yi, yanzu wasu dalibai sun gwammace shiga aikata laifuka, yayin da wasu kuma suka zama kamar wadanda ba su taba yin karatu ba. Duk da haka akwai wadanda har yanzu ba su fid da ran abubuwan da suka shafi ilimi na iya gyaruwa a Nijeriya.

Bugu da kari, binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara yajin aikin ASUU na farko a shekarar 1988, lokacin da ta yi zanga- zanga dangane da mulkin Janar Ibrahim Badamasi Babangida wajen samun albashin da ya dace da kuma ba ta ‘yancin da ya dace. Hakan shi ya sa aka soke kungiyar ASUU a ranar 7 ga Agustan 1988 tare da kwace duk wasu kaddarorinta.

An ba ta damar sake ci gaba da harkokinta a 1990, sai dai bayan wani yajin aikin an sake soke kungiyar a ranar 23 ga Agustan 1992.

Amma bayan wata yarjejeniyar da aka cimma a ranar 3 ga Satumban 1992 wanda aka biya hakkokin kungiyar masu yawa da suka hada da damar da ma’aikata suke da ita na zauna da su wajen tattauna bukatunsu.

Duk korafi da maganganun da kungiyar ASUU suke yi dangane da yajin aiki, abin ya fi maida hankali ne kan kudaden da ake ba su da kuma gyara a jami’oin gwamnati har ma da wasu alawus da ta ce ariyas na kudaden sun kai naira biliyan 92 a wancan lokacin.

A halin ake ciki yanzu kudaden sun wuce haka, saboda kudaden ariyas din da suke bi ba a biya su ba tun daga shekarar 2016.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben 2023: Kwankwaso Ya Cancanta Ya Shugabanci Nijeriya -Zakiru Kusfa

Next Post

Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

Related

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

2 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 week ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

1 month ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

2 months ago
Next Post
Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

June 2, 2025
2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

2027: Ƙungiyar Shekarau Ta Gindaya Sharaɗi Kafin Shiga Haɗakar Jam’iyyu

June 2, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.