ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Da Daliban Jami’o’i Suka Tafka Sakamakon Yajin Aikin ASUU

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
ASUU

Daliban jami’o’in Nijeriya an tilasta masu rasa karatu har na tsawon shekara hudu wannan sakamakon yawan yajin aikin da Kungiyar Malaman jami’o’i ta Kasa (ASUU), suke tafiya tun lokacin da aka dawo mulkin farar hula gadan- gadan a shekarar 1999.

Binciken da Jaridar LEADERSHIP ta yi ya nuna yajin aikin da kungiyar ASUU take yi a halin yanzu shi ne na goma 16 tun da Nijeriya ta koma mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999.

  • Ma’aikatan Jiragen Sama Za Su Rufe Filayen Jirage Don Nuna Goyan Bayansu Ga ASUU A Yajin Aikin Da Suke

An rufe jami’o’in gwamnati fiye da shekaru 4 cikin shekara 23, wanda lokaci ne da ya kamata a ce an kammala karatun digiri, yayin da ake samun yajin aikin da yake kai makonni, wani yajin aikin kuma yake kai watanni.

ADVERTISEMENT

Yawan yajin aiki mai dadewa da kungiyar ASUU take yi abu ne wanda yake damun dalibai, iyayensu, da kuma masu ruwa da tsaki kan al’amarin da ya shafi ilmi.

Shekaru da yawa jami’o’in Nijeriya sun sha fuskantar matsaloli na rashin ba su kudaden da suka kamata a ba su don gudanar da ayyukansu. Ga dai kuma rashin isassun kayan da suka dace a ce suna amfani da su, wannan kuma abin an dade ana fuskantar hakan tun daga gwamnatocin da suka shude, abin har yanzu an rasa yadda za a maganin al’amarin.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

ASUU kungiya ce ta ma’aikata wadda aka kafa ta shekarar 1978 domin ta kare muradan malaman jami’o’in gwamnatin tarayya da na Jihohi, saboda kuwa babbar manufarsu ita ce kare mutuncinsu da kuma mu’amala tsakanin malaman jami’o’i da wadanda suka daukesu aiki, al’amarin da kullum yana kasancewa zaman doya da manja.

A karskashin mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, dalibai da ke karatu a jami’o’in Nijeriya sun rasa zagon karatu na watanni 13.

Hakan ya faru ne sanadiyar yajin aikin da Kungiyar ASUU ke tsunduma. Shi ya sa kwararru a bangaren ilimi suke cewa wadanda suka kammala karatunsu a jami’o’in Nijeriya, ba a daukarsu da wata daraja kamar wadanda suka yi karatu a kasashen waje.

Karkashin mulkin Shugaban Kasa Buhari, kungiyar ta fara shiga yajin aiki ne a ranar 17 ga Agustan 2017, bayan da gwamnati ta ki cika masu alkawarin da suka sa hannu a yarjejeniyar da suka yi.

Daga cikin fiye da naira tiriliyan daya da ASUU ta bukaci a ba ta, naira biliyan 200 ne kadai aka ba ta wannan kuma shi ne ya sa kungiyar ta shiga yajin aikin gargadi a watan Nuwamba 2016, domin a biya masu bukatunsu. An koma aiki ne a watan Satumba 2017.

Yajin aikin kungiyar ASUU na biyu an fara shi ne ranar 4 ga Nuwamban 2018, wanda ya kai zuwa 7 ga Fabarairun 2019, an yi kwana 95, wannan kuma ya faru ne sakamakon wasu al’amuran da ba a gama da su ba tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar na yarjejeniya da aka sa hannu ga bangarorin biyu a shekarar 2013.

A yanzu haka dai, sanadiyar yajin aikin ASUU, Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) za ta fara zanga- zangar goyon bayan a ranar 26 ga watan Yulin 2022.

Kungiyar ta ce babbar matsalar ita ce, rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya ta sa hannu da maganar aiwatar da su a shekarar 2019, domin kuwa dukkan jami’an gwamnati da na kungiyar sun amince da hakan.

Wadannan kuma sun hada da wani tsarin biyan su albashi da alawus da jin dadinsu da samun ‘yancin kan da ya shafi harkokin koyarwa da dai sauran su.

Bugu da kari binciken LEADERSHIP ya gano cewa saboda yawan tafiya yajin aiki da kungiyar take yi, yanzu wasu dalibai sun gwammace shiga aikata laifuka, yayin da wasu kuma suka zama kamar wadanda ba su taba yin karatu ba. Duk da haka akwai wadanda har yanzu ba su fid da ran abubuwan da suka shafi ilimi na iya gyaruwa a Nijeriya.

Bugu da kari, binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara yajin aikin ASUU na farko a shekarar 1988, lokacin da ta yi zanga- zanga dangane da mulkin Janar Ibrahim Badamasi Babangida wajen samun albashin da ya dace da kuma ba ta ‘yancin da ya dace. Hakan shi ya sa aka soke kungiyar ASUU a ranar 7 ga Agustan 1988 tare da kwace duk wasu kaddarorinta.

An ba ta damar sake ci gaba da harkokinta a 1990, sai dai bayan wani yajin aikin an sake soke kungiyar a ranar 23 ga Agustan 1992.

Amma bayan wata yarjejeniyar da aka cimma a ranar 3 ga Satumban 1992 wanda aka biya hakkokin kungiyar masu yawa da suka hada da damar da ma’aikata suke da ita na zauna da su wajen tattauna bukatunsu.

Duk korafi da maganganun da kungiyar ASUU suke yi dangane da yajin aiki, abin ya fi maida hankali ne kan kudaden da ake ba su da kuma gyara a jami’oin gwamnati har ma da wasu alawus da ta ce ariyas na kudaden sun kai naira biliyan 92 a wancan lokacin.

A halin ake ciki yanzu kudaden sun wuce haka, saboda kudaden ariyas din da suke bi ba a biya su ba tun daga shekarar 2016.

ASUU
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

ASUU
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
ASUU
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.