ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asarar Da Daliban Jami’o’i Suka Tafka Sakamakon Yajin Aikin ASUU

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
ASUU

Daliban jami’o’in Nijeriya an tilasta masu rasa karatu har na tsawon shekara hudu wannan sakamakon yawan yajin aikin da Kungiyar Malaman jami’o’i ta Kasa (ASUU), suke tafiya tun lokacin da aka dawo mulkin farar hula gadan- gadan a shekarar 1999.

Binciken da Jaridar LEADERSHIP ta yi ya nuna yajin aikin da kungiyar ASUU take yi a halin yanzu shi ne na goma 16 tun da Nijeriya ta koma mulkin dimokuradiyya a shekarar 1999.

  • Ma’aikatan Jiragen Sama Za Su Rufe Filayen Jirage Don Nuna Goyan Bayansu Ga ASUU A Yajin Aikin Da Suke

An rufe jami’o’in gwamnati fiye da shekaru 4 cikin shekara 23, wanda lokaci ne da ya kamata a ce an kammala karatun digiri, yayin da ake samun yajin aikin da yake kai makonni, wani yajin aikin kuma yake kai watanni.

ADVERTISEMENT

Yawan yajin aiki mai dadewa da kungiyar ASUU take yi abu ne wanda yake damun dalibai, iyayensu, da kuma masu ruwa da tsaki kan al’amarin da ya shafi ilmi.

Shekaru da yawa jami’o’in Nijeriya sun sha fuskantar matsaloli na rashin ba su kudaden da suka kamata a ba su don gudanar da ayyukansu. Ga dai kuma rashin isassun kayan da suka dace a ce suna amfani da su, wannan kuma abin an dade ana fuskantar hakan tun daga gwamnatocin da suka shude, abin har yanzu an rasa yadda za a maganin al’amarin.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

ASUU kungiya ce ta ma’aikata wadda aka kafa ta shekarar 1978 domin ta kare muradan malaman jami’o’in gwamnatin tarayya da na Jihohi, saboda kuwa babbar manufarsu ita ce kare mutuncinsu da kuma mu’amala tsakanin malaman jami’o’i da wadanda suka daukesu aiki, al’amarin da kullum yana kasancewa zaman doya da manja.

A karskashin mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, dalibai da ke karatu a jami’o’in Nijeriya sun rasa zagon karatu na watanni 13.

Hakan ya faru ne sanadiyar yajin aikin da Kungiyar ASUU ke tsunduma. Shi ya sa kwararru a bangaren ilimi suke cewa wadanda suka kammala karatunsu a jami’o’in Nijeriya, ba a daukarsu da wata daraja kamar wadanda suka yi karatu a kasashen waje.

Karkashin mulkin Shugaban Kasa Buhari, kungiyar ta fara shiga yajin aiki ne a ranar 17 ga Agustan 2017, bayan da gwamnati ta ki cika masu alkawarin da suka sa hannu a yarjejeniyar da suka yi.

Daga cikin fiye da naira tiriliyan daya da ASUU ta bukaci a ba ta, naira biliyan 200 ne kadai aka ba ta wannan kuma shi ne ya sa kungiyar ta shiga yajin aikin gargadi a watan Nuwamba 2016, domin a biya masu bukatunsu. An koma aiki ne a watan Satumba 2017.

Yajin aikin kungiyar ASUU na biyu an fara shi ne ranar 4 ga Nuwamban 2018, wanda ya kai zuwa 7 ga Fabarairun 2019, an yi kwana 95, wannan kuma ya faru ne sakamakon wasu al’amuran da ba a gama da su ba tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar na yarjejeniya da aka sa hannu ga bangarorin biyu a shekarar 2013.

A yanzu haka dai, sanadiyar yajin aikin ASUU, Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) za ta fara zanga- zangar goyon bayan a ranar 26 ga watan Yulin 2022.

Kungiyar ta ce babbar matsalar ita ce, rashin cika alkawarin da gwamnatin tarayya ta sa hannu da maganar aiwatar da su a shekarar 2019, domin kuwa dukkan jami’an gwamnati da na kungiyar sun amince da hakan.

Wadannan kuma sun hada da wani tsarin biyan su albashi da alawus da jin dadinsu da samun ‘yancin kan da ya shafi harkokin koyarwa da dai sauran su.

Bugu da kari binciken LEADERSHIP ya gano cewa saboda yawan tafiya yajin aiki da kungiyar take yi, yanzu wasu dalibai sun gwammace shiga aikata laifuka, yayin da wasu kuma suka zama kamar wadanda ba su taba yin karatu ba. Duk da haka akwai wadanda har yanzu ba su fid da ran abubuwan da suka shafi ilimi na iya gyaruwa a Nijeriya.

Bugu da kari, binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara yajin aikin ASUU na farko a shekarar 1988, lokacin da ta yi zanga- zanga dangane da mulkin Janar Ibrahim Badamasi Babangida wajen samun albashin da ya dace da kuma ba ta ‘yancin da ya dace. Hakan shi ya sa aka soke kungiyar ASUU a ranar 7 ga Agustan 1988 tare da kwace duk wasu kaddarorinta.

An ba ta damar sake ci gaba da harkokinta a 1990, sai dai bayan wani yajin aikin an sake soke kungiyar a ranar 23 ga Agustan 1992.

Amma bayan wata yarjejeniyar da aka cimma a ranar 3 ga Satumban 1992 wanda aka biya hakkokin kungiyar masu yawa da suka hada da damar da ma’aikata suke da ita na zauna da su wajen tattauna bukatunsu.

Duk korafi da maganganun da kungiyar ASUU suke yi dangane da yajin aiki, abin ya fi maida hankali ne kan kudaden da ake ba su da kuma gyara a jami’oin gwamnati har ma da wasu alawus da ta ce ariyas na kudaden sun kai naira biliyan 92 a wancan lokacin.

A halin ake ciki yanzu kudaden sun wuce haka, saboda kudaden ariyas din da suke bi ba a biya su ba tun daga shekarar 2016.

ASUU
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

Mataimakin Kwanturola Da Ke Kula Da Gidan Yarin Kuje Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.