• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga jama’ar Jihar Neja da sauran ‘yan Nijeriya da su tuno da shekaru 16 na mulkin PDP kuma su kwatanta su da shekaru bakwai na mulkin gwamnatin APC da ya kawo matsananciyar damuwa da talauci da rashin tsaro acikin al’ummar Nijeriya. 

 

Daga nan ya yi kira ga ‘ya’yan jihar da ma ‘yan Nijeriya baki ɗaya da su tabbatar sun aje kyakkyawan tarihi da kyautata wa ‘yan baya ta hanyar korar gwamnatin APC ta hanyar ƙin zaɓen dukkan ‘yan takarar ta a zaɓuɓɓukan da za a yi a watan gobe.

  • 2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

Atiku ya yi wannan kalamin ne a wajen taron yaƙin neman zaɓen PDP da aka yi a Minna, babban birnin Jihar Neja, a ranar Asabar.

 

Labarai Masu Nasaba

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

Akwai alamun cewa filin Kasuwar Bajekoli da ke unguwar Shango a garin Minna bai taɓa ganin dandazon mutane ba irin wanda ya gani a ranar Asabar wajen karɓar baƙuncin Atiku da Gwamna Arthur Ifeanyi Okowa na Jihar Delta.

 

Rundunar yaƙin neman zaɓen Atiku/Okowa ta isa Minna ne a ranar Asabar inda jama’a su ka yi dafifi domin tarbar su ta yadda filin ya cika ba masaka tsinke.

 

Tun misalin ƙarfe 8 na safe magoya bayan jam’iyyar su ka cika filin Kasuwar Bajekolin, a yayin da wasu kuma su ka nufi babban filin jirgin sama na Minna mai nisan kimanin kilomita daga cikin gari domin tarbar Atiku da Okowa, da kuma sauran manyan baƙi da su ka haɗa da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Abubakar Bukola Saraki, Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sokoto, Gwamnan Jihar Akwa Ibom, Emmanuel Udom, da tsofaffin gwamnoni Boni Haruna na Adamawa, Liyel Imoke na Kuros Riba, Malam Ibrahim Shekarau na Kano, da sauran su da dama.

 

Filin Kasuwar Bajekolin da ke Shango ya cika maƙil da dubban magoya bayan jam’iyyar PDP. Wasu ma daga wajen filin su ka tsaya, wanda hakan ya jawo cinkoson motoci cika a kan manyan hanyoyin Minna.

 

Tsohon gwamnan Neja, Dakta Mu’azu Babangida Aliyu (Talban Minna), wanda shi ne shugaban rundunar yaƙin neman zaɓen PDP a jihar a zaɓen 2023, shi ma ya yi kira ga jama’a da su fitar da APC daga mulkin jihar domin, a cewar sa, ba ta tsinana komai ba sai jawo baƙin ciki da wahala ga jama’a.

 

Sauran waɗanda su ka yi jawabi a taron sun haɗa da mataimakin Atiku a takara, wato Gwamna Okowa, da Shugaban PDP na ƙasa, Dakta Iyorchia Ayu, da Gwamna Aminu Tambuwal, da Dino Melaye, da Gimbiya Rakiya Atiku (maiɗakin Atiku Abubakar) da Sanata Zaynab Kure, da shugaban PDP na Neja, Tanko Beji, da Gwamna Emmanuel Udom na Akwa Ibom, da sauran su, waɗanda kowannen su ya shawarci masu zaɓe a jihar da su fitar da APC daga mulkin jihar da ma tarayya.

 

An ƙawata taron da hawan raƙuma da dawakai da raye-rayen gargajiya da waƙoƙin mawaƙa irin su Naziru Sarkin Waƙa da sauran su.

 

A ƙarshe, Dakta Babangida Aliyu ya shirya wa Atiku da sauran jiga-jigan jam’iyya walimar cin abincin rana a gidan sa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: PDP Ta Bukaci Gaggauta Cafke Tinubu Kan Zargin Safarar Miyagun Kwayoyi

Next Post

Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Related

Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar
Da ɗumi-ɗuminsa

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

13 hours ago
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
Labarai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

18 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

3 days ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

4 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

6 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

7 days ago
Next Post
Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Wa'adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.