ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

Ya Yaba Wa Gwamna Makinde Na Oyo

by Musa Muhammad
3 years ago
atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana ƙudirinsa na ƙara wa gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi ƙarfin gudanar da mulkinsu idan an zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a watan gobe.

Atiku ya faɗi haka ne a taron yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar wanda aka yi a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, a ranar Alhamis.

A jawabinsa kan shirin da ya yi wa ƙasar nan a wajen taron, wanda aka yi a Zauren Mapo, Atiku ya ce a ƙarƙashin gwamnatinsa za a sake fasalin mulkin ƙasar nan ta yadda za a tabbatar da cewa an ƙara wa gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi ikon gudanar da mulki.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Ya ce, “An san mutanen yankin Kudu-maso-yamma da neman a sauya fasalin ƙasar nan. Idan an ce sauya fasali, muna nufin a ba da ƙarin ikon mulki ga jihohi da ƙarin kuɗi. Ko kun fahimci hakan? Ko kun amince da a yi hakan?

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Yana daga cikin ginshiƙai biyar na shirye-shiryenmu don mu aiwatar da sauyin fasalin ƙasar nan — manufa ita ce mu ba ku ƙarin kuɗi da ƙarin ikon mulki ta yadda za ku iya haɓaka yankunan ku da jihohin ku da ƙananan hukumomin ku. Wannan shi ne mu ka sa a gaba.

Atiku
“Haka kuma, mun ƙudiri aniyar tabbatar da ba za a ƙara yin yajin aiki a jami’o’in mu ba — manufa za mu ba jami’o’in mu isassun kuɗi tare da biyan malaman mu a kan lokaci ta yadda ba za mu samu wani cikas a harkokin ilimin mu ba.

“Tilas mu tabbatar da cewa mun rungumi kowa da kowa. Kowane ɓangare na ƙasar nan zai samu wakilci a gwamnatin mu.

“Haka kuma mun ƙudiri aniyar tabbatar da mun samar da tsaron ƙasar mu don tabbatar da an samu kwanciyar hankali, tare da bin doka da oda a kowane ɓangare na ƙasar nan. Wannan shi ne abin da mu ka ƙudirta.”

Bugu da ƙari a jawabin nasa, Atiku ya yaba wa Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo kan yadda ya tabbatar da cewa taron yaƙin neman zaɓen ya shiryu sosai.

Duk da yake gwamnan bai halarci taron ba, Atiku ya ce, “Jama’ar Jihar Oyo, bari in yi amfani da wannan damar in ƙara yin godiya ga Gwamna Makinde da jam’iyyar PDP reshen Jihar Oyo saboda yadda su ka tabbatar da cewa wannan taron ya shiryu matuƙa kuma an yayata shi sosai.”

Shi ma Shugaban PDP na ƙasa, Dakta Iyorchia Ayu, wanda ya yi jawabi a wajen taron, ya yaba wa Makinde saboda “nasarar da aka samu” a wajen kamfen ɗin jam’iyyar a jihar.

Makinde dai ya na cikin gwamnonin nan na PDP guda biyar waɗanda ake kira G5, wato waɗanda su ka ware kan su daga kamfen ɗin da Atiku ke yi a faɗin ƙasar nan.

Sun yi hakan ne bisa kasa samun biyan buƙatar su ta lallai sai Ayu ya yi murabus daga kujerar sa ta shugaban jam’iyyar na ƙasa.

Gwamnonin su ne Nyesom Wike na Ribas, Ifeanyi Ugwuanyi na Inugu, Samuel Ortom na Binuwai, Seyi Makinde na Oyo, da Okezie Ikpeazu na Abiya.

atiku
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Messi Ya Fi Maradona A Argentina –In Ji Kocinsa

Messi Ya Fi Maradona A Argentina –In Ji Kocinsa

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.