ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko

Ya Yaba Wa Gwamna Makinde Na Oyo

by Musa Muhammad
3 years ago
atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana ƙudirinsa na ƙara wa gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi ƙarfin gudanar da mulkinsu idan an zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a watan gobe.

Atiku ya faɗi haka ne a taron yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar wanda aka yi a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, a ranar Alhamis.

A jawabinsa kan shirin da ya yi wa ƙasar nan a wajen taron, wanda aka yi a Zauren Mapo, Atiku ya ce a ƙarƙashin gwamnatinsa za a sake fasalin mulkin ƙasar nan ta yadda za a tabbatar da cewa an ƙara wa gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi ikon gudanar da mulki.

ADVERTISEMENT
  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

 

Ya ce, “An san mutanen yankin Kudu-maso-yamma da neman a sauya fasalin ƙasar nan. Idan an ce sauya fasali, muna nufin a ba da ƙarin ikon mulki ga jihohi da ƙarin kuɗi. Ko kun fahimci hakan? Ko kun amince da a yi hakan?

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Yana daga cikin ginshiƙai biyar na shirye-shiryenmu don mu aiwatar da sauyin fasalin ƙasar nan — manufa ita ce mu ba ku ƙarin kuɗi da ƙarin ikon mulki ta yadda za ku iya haɓaka yankunan ku da jihohin ku da ƙananan hukumomin ku. Wannan shi ne mu ka sa a gaba.

Atiku
“Haka kuma, mun ƙudiri aniyar tabbatar da ba za a ƙara yin yajin aiki a jami’o’in mu ba — manufa za mu ba jami’o’in mu isassun kuɗi tare da biyan malaman mu a kan lokaci ta yadda ba za mu samu wani cikas a harkokin ilimin mu ba.

“Tilas mu tabbatar da cewa mun rungumi kowa da kowa. Kowane ɓangare na ƙasar nan zai samu wakilci a gwamnatin mu.

“Haka kuma mun ƙudiri aniyar tabbatar da mun samar da tsaron ƙasar mu don tabbatar da an samu kwanciyar hankali, tare da bin doka da oda a kowane ɓangare na ƙasar nan. Wannan shi ne abin da mu ka ƙudirta.”

Bugu da ƙari a jawabin nasa, Atiku ya yaba wa Gwamna Seyi Makinde na Jihar Oyo kan yadda ya tabbatar da cewa taron yaƙin neman zaɓen ya shiryu sosai.

Duk da yake gwamnan bai halarci taron ba, Atiku ya ce, “Jama’ar Jihar Oyo, bari in yi amfani da wannan damar in ƙara yin godiya ga Gwamna Makinde da jam’iyyar PDP reshen Jihar Oyo saboda yadda su ka tabbatar da cewa wannan taron ya shiryu matuƙa kuma an yayata shi sosai.”

Shi ma Shugaban PDP na ƙasa, Dakta Iyorchia Ayu, wanda ya yi jawabi a wajen taron, ya yaba wa Makinde saboda “nasarar da aka samu” a wajen kamfen ɗin jam’iyyar a jihar.

Makinde dai ya na cikin gwamnonin nan na PDP guda biyar waɗanda ake kira G5, wato waɗanda su ka ware kan su daga kamfen ɗin da Atiku ke yi a faɗin ƙasar nan.

Sun yi hakan ne bisa kasa samun biyan buƙatar su ta lallai sai Ayu ya yi murabus daga kujerar sa ta shugaban jam’iyyar na ƙasa.

Gwamnonin su ne Nyesom Wike na Ribas, Ifeanyi Ugwuanyi na Inugu, Samuel Ortom na Binuwai, Seyi Makinde na Oyo, da Okezie Ikpeazu na Abiya.

atiku
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Messi Ya Fi Maradona A Argentina –In Ji Kocinsa

Messi Ya Fi Maradona A Argentina –In Ji Kocinsa

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.